Latest posts

First Page  |  «  |  1  |  2  |  3  |  4  |  5  |  6  ...  24  |  »  |  Last Search found 237 matches:


nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

ADDININ GASKIYA (1)

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:42 PM

ADDININ GASKIYA (1)(SAHABBAN MANZON ALLAH(SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAMA) DA ALAYENSA)Bismillahir Rahmanir Raheem. Wa Sallallahu ‘alan Nabiyyil Kareem, Wa ‘ala alihi wa Sahbihi wa man tabi’ahum bi ihsanin ila Yaumid-Din.ABIN DA AKE NUFI DA “SAHABI”:A harshen larabci idan aka ce “Sahib” yana daukar ma’anar: Aboki, Mabiyi, Wanda ya danfaru da mutum, ya lazimceshi, ko kuma wanda ya gamu da mutum.A ma’ana ta shari’a kuwa idan aka ce “Sahabi”, ana nufin:( WANDA YA GAMU DA ANNABI (SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAMA), YA YI IMANI DA SHI, YA KUMA MUTU A CIKIN ADDININ MUSULUNCI).Kenan ba za’a kira mutum “Sahabi” ba, sai ya cika sharuda guda uku:SHARADI NA DAYA: Gamuwada Annabi (Sallallahu alaihi wa sallama):Wannan gamuwa tana baiwa mutum daraja ta kasancewarsa “Sahabi”, sawa’un sun gamu kuma ya zauna da Ma’aiki zamani mai tsawo, ko kuma sau daya ne kurum gamuwar ta kasance. Idan dai har ya hadu da shi ko yaya ne, kuma ya cika ragowar sharudan da zamu ambata, to ya zama Sahabi.Akwai wata fahimta ta wasu malamai da suke ganin ba za’a ce wa mutum “Sahabi” ba, har sai ya dauki lokaci mai tsawo tare da Ma’aiki (SallalLahu alaihi wa sallama).Sai dai wannan fahimta ta sabawa ma’anar kalmar “Sahib” a harshen larabci; domin kuwa harshe bai bayyana irin wannan bambancin ba.Don haka, abin da ya fi rinjaye shine: ko da sau dayane tak gamuwar ta kasance to za’a kira mutum “Sahabi”.Wannan shi ya sanya don malamai su kara fito da ma’anar “Sahabi” fili, sabaninwaccan fahimtar sai suka ce Sahabi shine:“DUK WANI DA YA GAMU DAANNABI, KO DA SAU DAYA NE TAK, KO DA BASU YI IDO HUDU BA, KAMAR MAKAHO”.Daga nan suka kawo ragowarsharudan.Misalin wanda ba su yi ido hudu da Ma’aiki ba, amma kuma sun gamu daga cikin Sahabbai shine: Abdullahi bnUmmi Maktum (Allah ya karamasa yarda), shi makaho ne, bai taba ganin Ma’aiki da idanuwansa ba, amma kuma sahabi ne shi, saboda ya hadu da Annabi SallalLahu alaihi wa sallama.A takaice wannan sharadi ya nuna mana cewar wadanda suka riski zamanin Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama), amma ba su gamu da shi ba, suka ci gaba da zama a garuruwansu, kamar wasu da suke Sham ko Misra, ko Yaman… da sauransu…Ko kuma wadanda suka yi Imani da shi, suka kamo hanya don su yi mubaya’a, kafin su karaso Madina Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama) ya yi wafati, wadannan ba za’a kirasu “Sahabbai” ba. Ana kiran irin wadannan mutanen: “Mukhadhramun”; wato wadanda suka rayu a zamanin da aka aiko Ma’aiki, suka rayu har bayan wafatin Ma’aikin, amma basu samu darajar zama “Sahabbai” ba.SHARADI NA BIYU: IMANI:Dole mutumin da ya gamu da Ma’aiki (SallalLahu alaihi wa sallama) ya zamo ya yi Imani da shi, sa’annan ya samu siffa ta Sahabi.Wannan sharadi na biyu, wato yin Imani da Ma’aiki SallalLahu alaihi wa sallama ya fitar da Kafirai wadanda suka hada zamani da fiyayyen halitta, Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama), wadannan ba za su shiga cikin Sahabbai ba.Hakama wadanda suka gamuda shi, amma ba su yi imani da shi ba sai bayan wafatinsa, suma ba za a kidaya su cikin Sahabbai ba.Sannan Imanin dole ya zamoingantacce; don haka munafukai da suka kasance azamanin Manzon Allah SallalLahu alaihi wa sallama, irinsu Abdullahi bn Ubayyi bn Salul, ba zasu shiga cikin lissafin sahabbai ba, domin kuwa a zahiri ne suke bayyana cewa su musulmi ne, amma a boye ba haka bane.SHARADI NA UKU: DAWWAMA A CIKIN MUSULUNCI HAR MUTUWAWato Ya zamo wanda ya gamu da Ma’aiki SallalLahu alaihi wa sallama, ya kuma yiImani da shi, ya ci gaba da rike addinin musulunci har zuwa mutuwarsa, bai yi riddaya bar musulunci ba.Wannan sharadi ya fitar da jama’ar da suka yi ridda, wadanda Sayyidina AbubakarSiddik (Allah ya kara musu yarda) ya yi fama da su a farkon halifancinsa.Wadansu daga cikin wadannan jama’a da suka yi ridda, sun gamu da Ma’aki (SallalLahu alaihu wa sallama), kuma sun karbi musulunci a lokacin da yake a raye, sai dai bayan rasuwarsa sun fita daga addinin Allah, don haka ba zasu zamo cikin lissafin Sahabbai ba.FADAKARWA GUDA BIYU:1- Ridda itace: Mutum ya zo da wani abu da zai fitar da shi daga addinin musulunci, da furuci, ko kudurcewa, ko aiki. sawa’un ya yi hakan ne don izgilanci ga addini, ko don bijirewa, ko kuma kudurce hakan ya yi. Daga cikin misalan ridda: ya yi musun cewa akwai Allah, ko ya musa wani daga cikin manzanni, ko karyata su, ko ya halalta abin da aka haramta shi a Ijma’in malamai, ko ya haramta abinda yake halal ne a Ijma’i, ko ya yi niyyar cewa zai kafurta nan gaba. [Duba Minhaj na Nawawi: 1/427].2- Adadin Sahabban Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama) da suka halarci “Bai’atur Ridhwan” mutum Dubu daya da Dari Hudu ne (1400). Adadin wadanda Ma’aiki ya fita da su don bude Makka kuma sun kai, Dubu Goma (10,000). Wadanda suka halarci hajjin ban kwana tare da shi kuwa sun kai Dubu Dari, da Dubu Ashirin da Hudu (124,000). Wannan itace shahararriyar maganar malaman Sirah.ADDININ GASKIYA (2)(SAHABBAN MANZON ALLAHSALLALLAHU ALAIHI WA SALLAMA DA ALAYENSA)Ci gaba …Allah Mai girma da daukaka a cikin Kur’aninsa Mai tsarki ya yi bayanin girman daraja da tsarkaka ta mahaifar Manzon rahama, wato garin Makkah mai alfarma.Kamar yadda kuma ya yi bayanin siffofin Sahabban Annabi (SallalLahu alaihi wa sallama) a cikin AlKur’ani maigirma, da yadda siffofin nasusuke a cikin Attaura da Linjila. Yo Dama kuma ai hankali ba zai taba karbar cewa a bayyana girman daraja da matsayi na gari, amma kuma a kasa bayanin daraja da girma na abokin zama dahulda.Idan ya zamo bigiren da aka aiko Manzon karshen zamaniyana da wata kebantacciyar daraja, to lallai kuwa wadanda suka fi cancantar su samu matsayi da daraja kebantacciya sune Sahabbansa, wadanda suke tare da shi, dare da rana, (Allah ya kara musu yarda).Idan mutum ya taba zama dawani malami, mai kima, ya dauki karatu a wajensa, to yana daga cikin abin da al’ada ta gudana akai shine idan ana so a kwarzanta wannan mutumin, a bayyanakimarsa, da falalarsa, a lokacin da ake bayar da tarihinsa akan bayyana cewa har ya dauki karatu ma a wajen malami wane. Sai zaman da ya yi tare da wannan malamin ya zamo cikin abubuwan da suke karawa mutumin nan girma da kwarjini a wajen jama’a.To ina ga wanda malaminsa, da karatunsa duk a gaban fiyayyen halitta ya dauke shi?Lallai daukakar ta wuce a kwatantata! Lallai girman ya kai matuka! Lallai albarkar ta yawaita!Don haka kasancewarsu “Sahabbai” kadai daraja ce da ta kera duk wani aiki da zaka iya tunanin ambato shi, hakan ne ma ya sanya wannan siffa ta “Sahabi” takelazimtar duk wanda ya samu wannan gagarumar falalar. Idan ka leka littattafan tarjamar daidaikunsu, zaka samu cewa siffa ta farko da ake ambatowa ga kowanne daya daga cikinsu shine cewa: “SAHABIN MA’IKI NE SHI”.Bayan wannan falala ta kasancewarsu Sahabban fiyayyen halitta, Allah Madaukakin sarki da kansa ya yi musu yabo da kirari a cikin littafinSa Mai girma, wannan yabo kuwa zai ci gaba da binsu har a nade kasa.Ayoyin da suka zo a cikin Kur’ani suke bayanin girman falalar wadannan jama’a da yabo da kirari garesu za’a iyakasa zaka iya kasasu kashi biyu:1) Ayoyin da suka yi yabo a garesu a dunkule.2) Ayoyin da suka yi yabo filla-filla.Za mu duba wasu daga cikin wadannan ayoyin, mu yi bayanin ma’anoninsu a takaice, amma kafin nan, zanfara da matashiya:MATASHIYA:Lokacin da aka aiko Fiyayyen halitta (SallalLahu alaihi wa sallama), wadanda suka yi Imani da shi a Makka yawancinsu marasa karfi ne, don haka kafirai suka dora musu karan-tsana, suka yi ta zaluntarsu. Su kuwa Sahabban Ma’aiki na farko suka daure, suka yi ta hakuri,daga karshe ma aka kore su daga garuruwansu, aka kwace dukiyoyinsu, duk da haka saboda neman yardar Allah suka hakura da duk wata tsangwama da aka yi musu, suka bar garinsu da gidajensu, da dukiyoyinsu, suka yi hijira, ba don komai ba sai don su marawa addinin Allah da ManzonSa baya, ba wai don cimma wata bukata tasu ta duniya ba, kamar yadda Allah Madaukaki ya ce:( ﻳﺒﺘﻐﻮﻥ ﻓﻀﻼ ﻣﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺭﺿﻮﺍﻧﺎً ﻭﻳﻨﺼﺮﻭﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ. ( ﺍﻟﺤﺸﺮ: 8 )Bayan sun isa garin Madina, sai ya zamo musulunci yana samun daukaka, yana kara karfi, ya fara kafa turakunsa.Sai wasu jama’a saboda tsoron karfin wannan addini,wasu kuma saboda hassada da bakin cikin zamowarsa karfen kafa gare su (Saboda ya toshe musu wasu abubuwa na jin dadi da suke tunanin a baya zasu samu badon zuwan musuluncin ba, kamar yadda Abdullahi bn Ubayyi bn Salul ya kasance ana daf da a nada shi ya zamo sarkin ‘yan Madina, ana cikin haka, katsam! Ma’aiki ya iso wannan gari mai hasken albarka, sai wannan ya dagula masa lissafi). Irin wadannan mutanen sai suka shiga rigarmusulunci da niyyar zasu yi masa zagon kasa, su wadannan jama’a su ake kira “Munafukai”.Musulunci ya samu gindin zama a Madina, ya kuma yi karfin da a baya bashi da shi.Ta daya bangaren kuma sai ya zamo yana fama da kalubale ta bangarori uku, maimakon kalubale ta bangare daya da ya yi fama da shi a Makka, wadannan bangarorin sune:1- Kafurai sun ci gaba da sanya kafar wando daya da duk wata da’awa ta musulunci, suka kullaci komai nasa, suka ci gaba da bin duk wani salo na dakile shi, da aibata shi, da hana jama’a sauraron da’awarsa.2- Yahudawa, wadanda suke zaune a garin Madina, hassada ta ci ta cinyesu, bayan kuma dalilin da ya sanya suka tare a wannan gari mai albarka shine sun karanto a littattafansu cewa shine garin da Annabin karshen zamani zai yo hijira zuwa gare shi. Yahudawa a Madina Kashi uku ne: A) Banu Kainuka’. B) Banu Kuraizah. C) Banun Nadheer.3- Munafukai, wadanda suka shiga rigar musulunci, suke yi masa zagon kasa, ayyukan wadannan munafukan na zagon kasa ya bayyana kuru-kuru a yakin UHUD da kuma yakin KHANDAK, kamar yadda Allah madaukakin sarki ya ba da labarisu da siffofinsu a wasu surori na Kur’ani, wanda nangaba zamu tabo manya-manyan siffofin, mu bayyanabambancin Sahabi da Munafuki, ba kamar yadda wasu suke nema karfi da yaji suyi kwado su cakudasu ba, alhali babu mahada; kowanne dayansu akwai bayaninsa a littafin Allah.Da yake wannan kashin na karshe (Wato munafukai) a zahiri suna nuna cewa suna tare da musulmai, suna rayuwa tare da su, wasunsu ma a boye suke ba a san cewa munafukai bane, sai wasu suka cakuda su da Sahabbai, suka kasa bambancesu.Akwai sinfi guda uku a cikin musulmai:NA FARKO: Wadanda aka riga aka sani yakinan cewa muminai ne, Allah ya yi bayaninsu. Wadannan sune Sahabban Ma’aiki (SallalLahualaihi wa sallama) da sannu zamu yi bayanin siffofin da Allah Madaukaki ya basu.NA BIYU: Wadanda aka sani yakinan cewa munafikai ne, wadannan ba za’a taba lissafa su cikin Sahabbai ba, su ma zamu kawo siffofinsu yadda Allah ya yi bayaninsu.NA UKU: Wadanda akwai rudani a kansu, wato babu bayanin ajin da za’a sanya su.(Kashi biyun farko babu matsala ko kadan a kansu, domin kuwa duk wanda aka tabbata yana daya daga cikinsu, to yanke za’a danganta shi zuwa kashin da yake.Matsalar kawai ta takaita ne a kashi na karshe, wadanda ba’a sansu ba, alhali kuma munafukai ne, to wadannan babu wani da zai iya yanke hukunci kai tsaye a kansu a kuma karba sai Nassi daga Kur’ani ko Hadisi.Siffofin da zamu yi bayaninsuna Sahabbai, wato muminai, da siffofin da zamu yi bayani na munafukai su zasu bamu damar gane wadanda aka samu rudani a cikin lamarin na su.Dadin wannan addinin namukenan, babu wani abu da akayi inda-inda cikin bayaninsa, don haka duk wanda ya shigacikin rudani to shi ya ruda kansa, ko kuma bai zurfafa bincike a Kur’ani ba. AlKur’ani Mai girma shine babban alkalinmu a cikin irinwannan hali, da kuma hadisan fiyayyen halitta (SallalLahu alaihi wa sallama).Don haka, duk wanda zai kawo wani rudu a irin wannan matsayin, ka nemi ya kawo maka bayani kuru-kuru daga Kur’ani ko Hadisi, idan ya kawo maka nassi maigamsarwa to babu makawa ayi aiki da shi, idan kuwa ya kama kame-kame, to kada ma ka bata lokacinka wajen sauraronsa.A DUNKULE:Allah Madaukaki ya bayyana Sahabbai, Muminai, ya yi bayanin siffofinsu. Ya kuma yi bayanin munafukai, ya bayyana siffofinsu.Munafuki ba Sahabi bane, saboda Allah ya bambance su inda yake cewa:( ﻭﻳﺤﻠﻔﻮﻥ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﺇﻧﻬﻢ ﻟﻤﻨﻜﻢ ﻭﻣﺎﻫﻢ ﻣﻨﻜﻢ ( ﺍﻟﺘﻮﺑﺔ: 56 )A wannan Aya Allah ya yi bayanin cewa Munafukai sukan yi rantsuwa cewar suna cikin Sahabban ManzonAllah (SallalLahu alaihi wa sallama), bayan kuma sam basu cikin Sahabban ManzonAllah.(NAN GABA ZAMU DUBA SIFFOFIN DA ALLAH YA BAIWA SAHABBAI (ALLAH YAKARA MUSU YARDA), DA KUMA KIRARI DA YABO DA YA YI MUSU, MU YI BAYANINCEWA DUK WANDA ALLAH YA YARDA DA SHI TO HAR ABADA BA ZAI DAWO KUMA YA YI FUSHI DA SHI BA, MU KAWO DALILAI AKAN HAKANIN SHA’ALLAH).FADAKARWA GUDA BIYU:1- Surorin da Allah ya ambaci muminai da kuma munafukai a Kur’ani sun hada da: Baqara, da Ali Imran, da Nisa’, da Ma’idah, da Ankabut, da Ahzab, da Fath, da Qitaal, da Hadeed, da Mujadalah, da Hashr, da Munafiquun … Haka yawancin surorin da suka sauka a Madina.2- Malaman ULUMUL QUR’AN sun ce:(Duk wata Sura ta Kur’ani da aka ambaci Munafikai a cikinta to wannan sura Madaniyya ce, sai suratul Ankabut ita kadai ita ce Makkiyyah).Sun ce kuma: (Duk wata Surata Kur’ani da aka yi muhawara da ma’abota littafi[Yahudawa da Nasara] to wannan sura Madaniyya ce).Na san za mu iya riskar dalilin hakan.

Reply

nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

adn gaskiya 2

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:39 PM

ADDININ GASKIYA (2)SAHABBAN MA’AIKI SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAMA DA ALAYENSA (AS)ﺣﺐ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ﻭﺍﻟﻘﺮﺍﺑﺔ ﺳُﻨَّﺔٌ ﺃَﻟْﻘَﻰ ﺑﻬﺎ ﺭﺑﻲ ﺇﺫﺍ ﺃﺣﻴﺎﻧﻲﻓﻜﺄﻧﻤﺎ ﺁﻝُ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﻭﺻﺤﺒُﻪ ﺭُﻭﺡٌ ﻳﻀﻢُّ ﺟﻤﻴﻌَﻬﺎ ﺟﺴﺪﺍﻥﻓﺌﺘﺎﻥ ﻋَﻘْﺪُﻫﻤﺎ ﺷﺮﻳﻌﺔُ ﺃﺣﻤﺪ ﺑﺄﺑﻲ ﻭﺃﻣﻲ ﺫﺍﻧﻚ ﺍﻟﻔِﺌَﺘَﺎﻥﻓﺌﺘﺎﻥ ﺳَﺎﻟِﻜَﺘَﺎﻥ ﻓﻲ ﺳُﺒُﻞ ﺍﻟﻬﺪﻯ ﻭﻫﻤﺎ ﺑﺪﻳﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﻗﺎﺋﻤﺘﺎﻥ .[ ﻧﻮﻧﻴﺔ ﺍﻟﻘﺤﻄﺎﻧﻲ]A rubutun da ya gabata, na dauki alkawarin zan tabo irin tarin yabo da kirari da Allah Madaukakin sarki ya yi wa Sahabban Manzon rahama (SallalLahu alaihi wa sallama)a cikin Kur’ani, sai dai zan nemi afuwar ‘yan uwa, domin kuwa zan dan karkata akala, na tabo daya jijjigen da nake so na yi magana a kai wato Alayen Ma’aiki SallalLahu alaihi wa sallama, wanda sune fiffike na biyu nawannan jirin gwanon. Bayan nan kuma sai na dawo na cika alkawarin da na daukar wa kaina Insha’Allah:ALAYEN ANNABI (SallalLahu alaihi wa sallama)Muna da kalmomi guda biyu a nan, (Aal, da kuma Annabi),don haka a ka’idance idan za’a bayar da ma’anar kalma ana yin bayanin kowace dayadaga cikinsu ne da farko, bayan nan sai a yi bayanin abin da suke nunawa idan anrab’asu da junansu, amma tunda kalma ta biyu wato “Annabi” shahararriya ce, ba ta bukatar sharhi, zan takaitaakan kalma ta farko wato: “Aal”.KALMAR: “ﺁﻝ ” A HARSHEN LARABCI:Gagga-gaggan malaman harshen larabci sun fadi maganganu guda biyu, dangane da asalin kalmar Aal:MAGANA TA FARKO: Kalmar ﺁﻝ ta samo asali ne daga kalmar ﺃﻫﻞ , don haka ma’anarsu daya ce, babu bambanci.Masu wannan magana, sun dauki lokaci mai tsayi suna tafaman sharhin yadda kalmomin nan guda biyu suka zamo masu asali daya, har daga karshe suka cimma matsaya. Sai dai duk da kokari, da sha tale-tale da suka yi; malamai da yawa sun raunana wannan ra’ayin nasu, kuma suka bayyana dalilai masu yawa na rashin yardar tasu ga abin da aka cimma. [Duba: Jala’ul Afham, na Ibnul Kayyim don karin bayani].MAGANA TA BIYU: Kalmar ﺁﻝkalma ce mai zaman kanta, kuma asalinta daga ﺍﻭﻝ ne; Bajimin malamin harshen larabci (Jauhari) shima ya kawo wannan kalmar ce a karkashin (alif, wau, lam-ara). Don haka kalmar daga ﺁﻝَ ﻳَﺆُﻭﻝُ ﺇِﺫَﺍ ﺭَﺟَﻊَ take, ma’anar ﺁﻝَ da hausa: ya dawo.Idan kuma aka ce ﺁﻝُ ﺍﻟﺮَّﺟُﻞِ to ma’anarsa: mutanen da suke komawa zuwa ga mutum, ake dangantasu zuwa gareshi, yake kula da lamuransu.Abisa wannan maganar, kalmar ﺁﻝ zaman kanta take, ba ta da dangantaka da kalmar ﺃَﻫْﻞ a asalin gininta.A bangaren ma’ana kuwa idan akace “ ﺁﻝُ ﺍﻟﺮﺟﻞ ” to malaman harshen larabci sun fadi cewa tana daukar wadannan ma’anoni masu zuwa:1) MUTUM DA KANSA: Kamar yadda yazo a wata kira’a fadin Allah Madaukakinsarki:( ﺳﻼﻡ ﻋﻠﻰ ﺁﻝ ﻳﺎﺳﻴﻦ )Wato Aminici ya tabbata ga Annabi Ilyas da kansa.2) MABIYAN MUTUM.3) MATARSA.4) MAKUSANTARSA (wato ‘yan’uwa)ALAYEN ANNABI SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAMA A SHARI’ANCE:Fadakarwa: (A shari’ance babu bambanci tsakanin ﺁﻝ ﺍﻟﺒﻴﺖ , da ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺒﻴﺖ , don hakakowace aka yi amfani da ita to zata bayar da ma’anar dayar)Malamai sun tattauna dangane da su wanene Alayen Annabi, kuma sun fitar da maganganu da yawa,zan takaita bisa maganganunda suka fi muhimmanci da karfi a cikinsu, sune maganganu guda uku:MAGANA TA FARKO (1):ALAYEN ANNABI (SAW) SUNE: DUKKAN WADANDA AKA HARAMTAWA CIN SADAKAWannan maganar itace ta Imam Shafi’i, da Ahmad, da kuma yawancin malaman musulunci.Sai dai an kara samun sabania tsakaninsu wajen ayyana wadanda aka haramta musu cin sadakar? Shahararrun maganganun nasu kuwa a wannan gabar guda biyu ne:1- Sune Banu Hashim da Banul Muddalib – (Wannan shine ra’ayin Imam Shafi’i kuma ruwaya ce daga Imam Ahmad).2- Sune Banu Hashim su kadai (Wannan shine ra’ayin Imam Abu Hanifa, itama wata ruwaya ce daga Imam Ahmad, Ibnul Kasim almajirin Imam Malik shima ya karkata zuwa wannan ra’ayin).KUMA WANNAN MAGANA TA BIYUN TA FI KARFIN HUJJA.Gaba dayan malaman kuma dalilan da suka rike akan cewa Alayen Annabi (SallalLahu alaihi wa sallama)sune wadanda aka haramtawa cin sadaka suna da yawa, ga kadan daga ciki:1). Hadisin da Bukhari ya ruwaito [Lamba: 1485] daga Abu Huraira yace: An kawo sadakar dabino tsibi guda wajen Annabi (SallalLahu alaihi wa sallam) sai Hasan da Husain suka rika wasa da dabinon, sai dayansu ya dauki kwaya daya ya sanya a bakinsa, sai Ma’aiki ya fitar da dabinon daga bakin nasa, yace: (Baka san cewa Alayen Muhammad ba su cin sadakaba!).2). Hadisin da Muslim ya ruwaito [Lamba: 2408] daga Zaid bn Arkam da tsawonsa, wanda a ciki ya jawo hankulan jama’a su kula da Ahlulbait. Daga karshe hadisin aka yi wa Zaid bn Arkam tambaya, su wanene “Ahlulbait” ne? sai yace: sunewadanda aka haramtawa cin sadaka, sune: Alu Aliy, da AluAkil, da Alu Ja’far, da Alu Abbas.3). Hadisin da Muslim ya ruwaito [Lamba: 1072] cewa Rabi’ah dan Harith, yace da Muddalib bn Rabi’ah da Fadhl bn Abbas, kuje wajen Manzon Allah, ku roke shi ya baku aikin karbo sadaka. A karshen hadisin Ma’aiki SAW yake ce musu: (Ai sadaka kazantar mutane ce, ba ta halatta ga Muhammad, ko kuma alayen Muhammad!).(Masu wannan magana suka ce: A wadannan hadisan, Ma’aiki SallalLahu alaihi wa sallama da kansa ya fassara mana abin da ake nufi da Ahlulbaiti; don haka za mu yi riko ne da fassarar Ma’aiki, saboda duk wata fassara da za’a yi kuma to lallai a bayan wannan take).Akwai karashen magana bisawannan gab’ar nan gaba …MAGANA TA BIYU (2):ALAYEN ANNABI (SAW) SUNE: ZURIYARSA (‘YA’YANSA) DA MATANSA:Suma masu wannan maganar suna da dalilai masu yawa, daga cikinsu:1). Fadin Annabi (SAW) a hadisin da Muslim ya ruwaito [Lamba: 407]:( ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺻﻞ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺃﺯﻭﺍﺟﻪ ﻭﺫﺭﻳﺘﻪ ﻛﻤﺎ ﺻﻠﻴﺖ ﻋﻠﻰ ﺁﻝﺇﺑﺮﺍﻫﻴﻢ ).Suka ce: fadinsa: “ ﻭﻋﻠﻰ ﺃﺯﻭﺍﺟﻪ ﻭﺫﺭﻳﺘﻪ ”, fassara ce ta hadisin da ya zo da lafazin: “ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻝ ﻣﺤﻤﺪ ”; saboda haka: Idan aka ce: Alayen mutum to ana nufin Matansada ‘ya’yansa.2). Akwai wani lokaci da Ma’aiki ya shiga gidansa ya yiwa matansa sallama da cewarsa:ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺒﻴﺖ ﻭﺭﺣﻤﺔ ﺍﻟﻠﻪKuma ruwayar ta nuna cewa matan nasa ya yi wa sallamar, kamar yadda Bukhari ya ruwato [Lamba: 4793].3). Yadda aka koro magana a cikin ayar Suratul Ahzab, ya nuna cewa matansa suna cikin Ahlulbait, inda Allah Madaukaki yace:( ﺇﻧﻤﺎ ﻳﺮﻳﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﻟﻴﺬﻫﺐ ﻋﻨﻜﻢ ﺍﻟﺮﺟﺲ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺒﻴﺖ )Siyakin maganar ya nuna kuru-kuru cewa da su ake, shi ya sanya don Ma’aiki ya nunawa al’umarsa cewa akwai wasu da suma suke shiga karkashin wannan ayar, kari a bisa matan nasa, sai ya bayyana haka a aikace a cikin hadisin kisa’ (mayafi) yayin da ya lullube Aliyu da Fadima, da Hasan, da Husain(Allah ya kara musu yarda).(Masu wannan magana ta biyu suka ce: Wadannan dalilan sun nuna mana karara cewa Matan Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama) sun shiga cikin kalmar Ahlulbait, kuma akwai wasu karin dalilan ma, sai dai zamu takaita bisa ukun da muka kawo).MAGANA TA UKU (3):ALAYEN ANNABI (SAW) SUNE: AL’UMARSA, WATO MABIYANSA HAR IZUWA RANAR TASHIN KIYAMAMasu wannan magana sun kafa hujja da fadin Allah Madaukakin sarki:) ﻭﺣﺎﻕ ﺑﺂﻝ ﻓﺮﻋﻮﻥ ﺳﻮﺀ ﺍﻟﻌﺬﺍﺏ .ﺍﻟﻨﺎﺭ ﻳﻌﺮﺿﻮﻥ ﻋﻠﻴﻬﺎ ﻏﺪﻭﺍ ﻭﻋﺸﻴﺎًّ ﻭﻳﻮﻡ ﺗﻘﻮﻡ ﺍﻟﺴﺎﻋﺔ ﺃﺩﺧﻠﻮﺍ ﺁﻝ ﻓﺮﻋﻮﻥ ﺃﺷﺪ ﺍﻟﻌﺬﺍﺏ ).Ma’ana: (Mummunar azaba ta sami mabiya Fir’auna. Wuta ce za’a rika bijirar da sugareta safe da yamma. Ranarda alkiyama za ta tashi kuma za’a ce: kushigar da mabiyan Fir’auna cikin azaba mai tsanani). [Gafir: 45-46]Alayen Fir’auna a wannan ayar kamar yadda muka ganisune mabiyansa.BAYAN HAKA ALLAH SHINE MASANI, Amma maganar da ta fi rinjayen hujja itace: wadda ta yi bayanin cewa alayen Manzon Allah (SAW) sune wadanda aka haramta musu cin sadaka, wadanda aka haramtawa cin sadakar KUMA sune banu hashim su kadai. su kuwa banul muddalib a ingantacciyar magana ba su cikin wadandaaka haramtawa cin sadaka.MATAN ANNABI (SAW) kuwasun shiga cikin alayen Ma’aikine saboda suna cikin huruminsa da dalilin ayar SURATUL AHZAB, ba wai a usuli suka kasance a cikinsu ba.Don haka, duba da abin da ya gabata, zamu fahimci cewa wadanda suka ci sunanALAYEN MA’AIKI (SAW) nau’i biyu ne:1- Alayen Ma’aiki TA USULI: Sune duk wani Bahashime.2- Alayen Ma’aiki TA DALILI: sune matan Ma’aiki, domin kuwa sun shiga ne dalilin auren Ma’aiki SAW, kafin ya aure su ba su cikin alayen nasa.FADAKARWA GUDA BIYU1- Banu Hashim sune ‘ya’yan Hashim dan abdu Manaf, kaka na biyu ga Ma’aiki (SAW), yana da ‘ya’ya guda biyu: Abdul Muddalib, da Asad. AbdulMuddalib ya haifi‘ya’ya maza guda goma. Shi kuma Asad yana da ‘ya’ya maza amma basu hayayyafa ba, yana kuma da ‘ya Mace mai suna Fadima, wadda itace mahaifiyar su SayyidinaAliyu RA.Don haka dukan ‘ya’yan da suka gangaro ta hanyar AbdulMuddalib da kuma ‘yar uwarsa Fadima su suka zamoBanu Hashim. Kamar yadda hadisin Zaid bn Arkam da ya gabata ya yi bayaninsu dalla-dalla. Su guda hudun nan da ya ambata sune bayansu bai yanke ba.2- Wasu suna da ra’ayin cewaalayen Manzon Allah sune kawai wadanda ya lullube su a cikin mayafi yace: (Wad’annan alayen gidana ne), wato: Aliyu da Fadima daHasan da Husain (Allah ya kara musu yarda) kamar yadda Tirmizi ya ruwaito [Lamba: 3787] daga Nana Ummu Salamah (Allah ya kara mata yarda).Haka ma sun kafa hujja cewaa lokacin MUBAHALA Ma’aiki yazo da su ne su kadai, don haka ya nuna cewa su kadai ne alayen gidan Ma’aiki.Sai dai takaita Alayen Ma’aiki a kan wadannan hudun su kadai saboda wadannan dalilan da suka ambato hanya ce mai rauni sosai, saboda dalilai masu zuwa:a). Duk musulmi ya tabbatar cewa wadannan hudun (Allah ya kara musu yarda) suna cikin Banu Hashim, donhaka babu kokwanton suna cikin Ahlulbait. Idan aka ce alayen Ma’aiki sune Banu Hashim to zai game wadannan hudun da wasu ma kari a kansu.b). A Hadisin Kisa’ (Mayafi) Ma’aiki yana nuna mana ne cewar wadannan hudun ma suna shiga karkashin ayar data zo take bayani bisa matan manzon Allah SAW; domin kuwa ba don Ma’aiki ya aikata hakan ba, babu wani da zai iya shigar da wasu karia kan matayen Manzo wadanda sune zahirin ayoyinsuke magana a kansu su kadai.c). Hadisai masu yawa da inganci da haske kamar rana,wanda babu kokwanto a cikinsu sun zo sun yi bayanincewa Ahlulbait sun fi hakan yawa, kamar yadda muka kawo wasu a sama.Don haka, kasancewar an samu wani hadisi ya takaita bisa ambaton mutum hudu kawai ba ya nuna cewa bayan su babu wasu.Bayanin haka kuwa shine: Hadisin kisa’ (mayafi) za’a dauke shi ne a matsayin ya ambaci wasu shashi daga cikin jumla masu yawa da suke dauke da wata siffa gaba dayansu, ya kuma basu hukunci iri daya da wanda yariga ya baiwa gaba dayan nasu.Malaman Usulul Fiqh suna cewa:ﺫِﻛْﺮُ ﺑﻌﺾِ ﺃﻓﺮﺍﺩ ﺍﻟﻌﺎﻡ ﺍﻟﻤﻮﺍﻓﻖ ﻟﻪ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﻜﻢ ﻻ ﻳَﻘْﺘَﻀﻲ ﺍﻟﺘﺨﺼﻴﺺَWato: Idan aka samu dalilin da hukuncinsa ya kunshi wasu jama’a da yawa, sai kuma aka samu wani dalili yaware wasu daidaiku daga cikin wadannan jama’ar, ya kara ba su irin wannan hukuncin da ya yi wa jama’ar,daidai wa daida; to keb’e daidaikun ba zai sanya a sarayar da wancan hukuncin wanda ya game su gaba dayaba, a’a duka biyunsu za su yi aiki a lokaci guda. Saboda babu wani cin karo tsakanin dalilan guda biyu. [duba: Nihayatus Sul, na Asnawi: 1/544, da Al-Bahrul Muheed na Zarkashi: 3/220 don karin bayani].BAYANI: Dalili yazo yace: Dukbanu Hashim Ahlulbaiti ne, sai kuma muka samu wani dalilin ya ware wasu daga cikin Banu Hashim din yace: wadannan Ahlulbaiti ne. To dukan dalilan biyu zasu yi aiki ba tare da matsala ba. Karamin ba zai kebance babban ba saboda babu cin karo, ko sabani tsakaninsu.‘KARIN FITO DA BAYANI:MISALI KACE: BANU HASHIMAHLULBAITI NE, SAI KUMA WANI LOKACI DABAN KA NUNA WASU DAGA CIKIN BANU HASHIM DIN KACE: WADANNAN AHLULBAITI NE.A’ina zamu iya fahimtar cewaakwai cin karo tsakanin wadannan bayanan guda biyu?!

Reply

nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

adn daskiya 3

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:37 PM

ADDININ GASKIYA (3)SAHABBAN MA’AIKI SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAMA DA ALAYENSAAlhamdu lilLah, Wassalatu Wassalamu ala rasulilLah, Wa ala Alihi wa Sahbihi, wa man tabi’ahum bi ihsanin ‘ila yaumid deen.A baya na yi alkawarin kawo bayanin irin girman kirari da yabo, da siffofi masu haske da Allah Mai girma da daukaka ya baiwa abokan zaman Ma’aiki (SallalLahu alaihi wa sallama), sai dai kafin wannan na tabo jijjige na biyu na unwanin wadannan maqalolin nawa wato alayen Ma’aiki (SallalLahu alaihi wa sallama).Ina kuma fatan a yanzu In sha’Allah babu wani abu da ya rage da zai shige mana duhu game da abin nufi da wadannan jama’a guda biyu (SAHABBAI DA ALAYE).DON HAKA, Yanzu zan shiga kai tsaye cikin abin da na yi alkawari, zan kuma dauki fitattun ayoyin alkur’ani da suka kunshi yabo da kirari gawadannan manyan bayin Allah na yi bayaninsu dalla-dalla, zan bi salon bayanin siffofin Sahabbai a karkashin kowace Aya da zan kawo, idan akwai munasaba zan kawo hadisai da maganganun malaman musulunci.Zan bayar da karfina bisa bayanin siffofin Sahabban Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama) ne kamar yadda Allah ya gaya mana su; domin da sanin siffofinsune zamu iya gane bambanci tsakaninsu da wasunsu (kamar Munafukan zamanin Manzon Allah), wadanda wasu jama’a, marasa adalci, masu fama da ciwon zuciya da tsatsarta suke ta kokarin sai sun gwamutsa tsakaninsu, sun basu hukunci guda daya, alhali Allah Madaukakin sarki da kansa ya riga ya sanya iyaka tsakaninsu, ba mai gane hakan kuwa sai wanda Allah ya datar, ya yalwata masa kirjinsa, ya bude basirarsa, ba wanda gilli da hassada, datsatsa suka cika zuciyarsa ba,suka hana shi sakat, ba shi son ya ji an ambaci wani abunasu na arziki, shi wannan duk yadda zaka yi dashi ba zai taba ganin haske ba, sai wani ikon Allah.( ﻭﻣﻦ ﻟﻢ ﻳﺠﻌﻞ ﺍﻟﻠﻪ ﻟﻪ ﻧﻮﺭﺍً ﻓﻤﺎ ﻟﻪ ﻣﻦ ﻧﻮﺭ )KIRARI DA YABO DA ALLAH YA YI WA SAHABBAN MA’AIKI A KUR’ANI:NA KASA AYOYIN KASHI UKU:1- Ayoyin da suka yi yabo da kirari ga jumullar Sahabban Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama).2- Ayoyin da suka yi yabo da kirari ga Sahabban Ma’aiki dasuke dauke da wata siffa, KAMAR MUHAJIRUN, DA ANSAR.3- Ayoyin da suka yi yabo da kirari ga wasu jama’a daga cikin Sahabban Manzon Allah(SallalLahu alaihi wa sallama)saboda nuna bajintarsu ta halartar yake-yake tare da Ma’aiki.NA FARKO: AYOYIN DA SUKE YABO DA KIRARI GA JUMULLAR SAHABBAN MA’AIKI SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAMA:Aya Ta Daya:fadin allah madaukakin sarki:ﻣﺤﻤﺪ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﺬﻳﻦ ﻣﻌﻪ ﺃﺷﺪﺍﺀ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻜﻔﺎﺭ ﺭﺣﻤﺎﺀ ﺑﻴﻨﻬﻢ ﺗﺮﺍﻫﻢ ﺭﻛﻌﺎً ﺳﺠﺪﺍً ﻳﺒﺘﻐﻮﻥ ﻓﻀﻼ ﻣﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺭﺿﻮﺍﻧﺎ، ﺳﻴﻤﺎﻫﻢ ﻓﻲ ﻭﺟﻮﻫﻬﻢ ﻣﻦ ﺃﺛﺮ ﺍﻟﺴﺠﻮﺩ، ﺫﻟﻚ ﻣﺜﻠﻬﻢ ﻓﻲﺍﻟﺘﻮﺭﺍﺓ ﻭﻣﺜﻠﻬﻢ ﻓﻲ ﺍﻹﻧﺠﻴﻞ ﻛﺰﺭﻉﺃﺧﺮﺝ ﺷﻄﺄﻩ ﻓﺂﺯﺭﻩ ﻓﺎﺳﺘﻐﻠﻆ ﻓﺎﺳﺘﻮﻯ ﻋﻠﻰ ﺳﻮﻗﻪ ﻳﻌﺠﺐ ﺍﻟﺰﺭﺍﻉﻟﻴﻐﻴﻆ ﺑﻬﻢ ﺍﻟﻜﻔﺎﺭ، ﻭﻋﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺁﻣﻨﻮﺍ ﻭﻋﻤﻠﻮﺍ ﺍﻟﺼﺎﻟﺤﺎﺕ ﻣﻨﻬﻢ ﻣﻐﻔﺮﺓﻭﺃﺟﺮﺍً ﻋﻈﻴﻤﺎً ).Ma’ana:([Annabi] Muhammadu Manzon Allah ne kuma wadanda suke tare da shi (masu) tsanani ne a kan kafirai, kuma masu tausayin junansu ne, za ka gansu sunaruku’i suna sujjada suna neman falala da yarda daga Allah, alamominsu suna cikinfuskokinsu na gurbin sujjada,wancananka misalinsu kenana cikin Attaura. Misalinsu kuma a cikin Linjila kamar shuka ce da ta fitar da tsakinta, ya karfafata, suka kuma yi kauri, suka daidaita a kan itatuwansu, har take baiwa manoma sha’awa; donkuma su fusata wadan da suka kafirta da su. Allah ya yiwa wadan da suka yi Imani, suka yi ayyuka na gari daga cikinsu alkawarin gafara da kuma lada mai girma). [Fath: 29].Allah Madaukaki ya bayar da misalin Annabi da Sahabbansa a cikin Attaurar Annabi Musa da Linjilar Annabi Isa.Misalinsu a cikin Attaura zahiri ne kamar yadda muka gani.Misalinsu kuwa a cikin Linjilaan misalta su da shuka wadda a farkonta take farawa rarrauna,’yar siririya, dan yaro ma zai iya tsige ta, saboda tsananin rauninta, bayan nan kuma sai ta yi ta yin tsiro tana fidda ressa, daga nan ta zo ta yi kauri ta yi karfi, ta yi kyau har tana kayatar da manoma, masanashuka.To haka Annabi SAW ya kasance da shi da Sahabbansa, a farkon musulunci sun kasance ‘yan kadan, masu rauni, bayan nan suka rika habaka, adadinsu na karuwa, har suka kai matsayin da suka kai, gaba dayan tsibirin larabawa ya rissina wa wannan addini, daga nan kuma ya fantsama zuwa dukkan fadin duniya. [duba: Adhwa’ul Bayan: 7/398].YADDA ALLAH MADAUKAKI YA SIFFAITA SAHABBAI A WANNAN AYA:A wannan ayar Allah ya yi bayanin wasu siffofi masu fantsamar haske na Sahabban Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama)kamar haka:1- MASU TSANANI NE BISA KAFURAIA wajen yakarsu, da nuna ba su tare da su, da gaba da su, wato suna fishi domin Allah, suna ki domin Allah. Mutum daga cikin Sahabbai yakan yaki Iyayensa ko ‘ya’yansa, ko‘yan uwansa na jini, ko wasu danginsa na kusa, duk dan daukaka kalmar Allah.Mun sani kuma SAHABBAN MANZON ALLAH LALLAI SUNSIFFANTU DA WANNAN SIFFA.2- MASU JIN KAN JUNANSU NESuna so da kaunar junansu saboda Allah. Ma’aiki ya bayar da labarin yadda muminai suke tausayawa junansu yake cewa: (Zaka samu muminai a wajen soyayya, da tausasawa, da jinkan junansu kamar misalin gangar jiki guda ne, idan wata gaba tana jin radadin ciwo, sai gaba dayan gangar jikin ta dauka tare da wannangabar tana taya ta jimami, ta hanyar rashin barci, da yin zazzabi). [Bukhari: 6011, Muslim: 2586].3- MASU YAWAN BAUTAR ALLAH NE:Zaka gansu suna ruku’i, suna sujjada. Aliyu (Allah ya kara masa yarda) yace: “Hakika ban ga wanda ya yi kama da Sahabban Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama)a cikinku ba: sun kasance suna wayar gari, kawunansu a tsefe, jikkunansu sun yi kura, sun kwana cikin sujjadada tsayuwar dare, aikinsu shine tsayuwar dare da yawan sujjada, idan suka mike kai kace akan garwashin wuta suke sabodatunawa da karshensu, tsakanin goshinsu ya yi kamar gwiwoyin tumakai saboda tsawaita sujjada, idan suka ambaci Allah sai idanunsu su kawo ruwa su cika da hawaye, su kadu kamar yadda iska take kada bishiya a ranar da ake iska mai tsananin karfi”. [Duba: “Al-Hilyah” ta Abu Nu’aim: 1/76, da “Nahjul Balaga” huduba ta 97].4- SUNA YIN DUKKAN AYYUKANSU DON NEMAN FALALAR ALLAH, WATO ALJANNA, DA KUMA YARDARSA:Ba suna yinsu ne don wani abin duniya ba, wannan kuwa siffa ce ta badini, ba wanda ya isa ya san hakan sai mahaliccinsu shi kadai, domin kuwa aiki ne na zuciya, gashi Allah ya shedi zukatansu yadda suke, don haka ba wanda ya isa ya bayar da wani labari akasin hakan a karba.5- SABODA YAWAN SALLAH IDAN MUTUM YA DUBA FUSAKURSU ZAI GA HASKEN GURBIN SUJJADA:Domin kuwa idan mutum ya inganta badininsa ga Allah, to sai Allah ya kyautata zahirinsa ga mutane, su rika ganin yana ta haske da annuri.6- ADADINSU KADAN NE A FARKON MUSULUNCI, AMMA DAGA BAYA, SUKA RIKA HABAKA, SUKA YI YAWA HAR SUKA KAI MATSAYIN DA SUKA KAI:Don haka duk masu cewa Sahabban Ma’aiki wasu ‘yan tsiraru ne kawai, da basu fi a kirge su a tafukan hannu biyu ba, sun ci karo da abin da Allah yake gaya mana na misalin Muhammadu da Sahabbansa a cikin Linjila. Sannan suna nuna mana cewar Ma’aiki ya gaza wajen baiwa wadanda suke tare da shi kyakkyawar tarbiyar da tadace. (WAL’IYAZU BILLAH!!)7- SUNA CUNKUSAWA KAFIRAI HAUSHI DA BAKIN CIKI:Ko yaushe kafirai ba su son jin labarinsu, ko a fadi wani ci gaba nasu, sunayensu ma kawai suna tayar musu da hankali.Don haka ne ma Imam Malik ya bayar da fatawar cewa Shi’awa Rafida, masu kin Sahabban Ma’aiki (SallalLahualaihi wa sallama) kafurai ne,saboda suna bakin ciki da sahabban Ma’aiki, babu mai yin bakin ciki da su kuwa sai kafuri. (Allah ya kiyashe mu!).Abu ‘Urwatuz Zubairi ya ruwaito cewa: Mun kasance a majalisin Imamu Malik bn Anas, sai aka yi maganar wani mutum da yake kushe Sahabban Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama)sai Imamu Malik ya karanto wannan ayar, har ya kai inda Allah yake cewa: ( ﻟﻴﻐﻴﻆ ﺑﻬﻢ ﺍﻟﻜﻔﺎﺭ ) daga nan yace: “Duk wani mutum da zai wayi gari a zuciyarsa yana jin wani bakin ciki kan daya daga Sahabban Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama)to ya shiga cikin wannan ayar). [Tafsirin Kurdubi: 16/297].Ya zo a hadisin Abu Sa’idil Khudri Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallama)yana cewa: (Akul Kada ku soma zagin Sahabbai na! domin kuwa na rantse da Sarkin da raina yake hannunsa, da dayanku zai bayar da sadakar zinaren da girmansa ya kai kwatankacin dutsen Uhud, to ladan da zai samu ba zai kai kwatankwacin ciyarwar da daya [daga Sahabbai na] zai yi na Mudu guda daya, ko rabinsa ma ba). [Bukhari: 3673, Muslim: 2541].ﺃﻭﻟﺌﻚ ﺃﺻﺤﺎﺏ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﻭﺣِﺰْﺑُﻪ ﻭﻟﻮﻻﻫﻢُ ﻣﺎ ﻛﺎﻥ ﻓﻲ ﺍﻷﺭﺽ ﻣﺴﻠﻢﻭﻟﻮﻻﻫﻢُ ﻛﺎﺩﺕ ﺗَﻤِﻴﺪ ﺑﺄﻫﻠﻬﺎ ﻭﻟﻜﻦ ﺭﻭﺍﺳﻴﻬﺎ ﻭﺃﻭﺗﺎﺩُﻫﺎ ﻫﻢُﻭﻟﻮﻻﻫﻢُ ﻛﺎﻧﺖ ﻇﻼﻣﺎً ﺑﺄﻫﻠﻬﺎ ﻭﻟﻜﻦ ﻫﻢُ ﻓﻴﻬﺎ ﺑُﺪُﻭﺭٌ ﻭﺃَﻧْﺠُﻢ[ ﻣﻴﻤﻴﺔ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ]Allah ya kara mana son Sahabban Manzon Allah, ya hada mu tare da su ranar Kiyama.FADAKARWA:Ina so a wannan ayar da kuma ayoyin da bayaninsu zai zo (In sha’Allah) mu mayar da hankali sosai wajen lissafo siffofin da AllahMadaukaki da kansa ya baiwa Sahabbai abokanen zaman Ma’aiki (SAW); domin daga baya zamu zo mu duba mu gani, shin wadannan siffofi sun yi daidai da na Munafukai da wasu masu ciwon zuciya suke so su gwamutsa su, ko kuma sun yihannun riga da su?Kada kuma mu manta masanin abin da yake na bayyane da na boye shine ya yi bayanin wadannan siffofi da Kansa (JALLA JALALUH!)AYA TA BIYU DA TAKE BAYANIN GIRMAN KIRARI DA YABO DA ALLAH MADAUKAKIN SARKI YA YI WA SAHABBAN MA’AIKI SAW, ITA CE FADIN ALLAH MAI GIRMA:( ﻛﻨﺘﻢ ﺧﻴﺮ ﺃﻣﺔ ﺃﺧﺮﺟﺖ ﻟﻠﻨﺎﺱ ﺗﺄﻣﺮﻭﻥ ﺑﺎﻟﻤﻌﺮﻭﻑ ﻭﺗﻨﻬﻮﻥ ﻋﻦ ﺍﻟﻤﻨﻜﺮ ﻭﺗﺆﻣﻨﻮﻥ ﺑﺎﻟﻠﻪ ).(Kun kasance al’uma mafi alheri da aka fitar wa mutane: kuna umarni da [aikata] alheri, kuma kuna hani ga mummunan aiki, kuma kuna yin Imani da Allah). [Al Imran: 110].Sahabban Ma’aiki (SAW) sune farkon wadanda suka shiga karkashin wannan ayar, saboda gare su aka fara fuskantar da maganar, Sahabbai sune mafi alheri dafalala fiye da duk wani karni da ya biyo bayansu; saboda Manzo shine fiyayyen manzanni, shiriyar da suke kai, babu wasu kafinsu da suke kan irinta.Ma’aiki SAW yace: (Mafi alheri cikin mutane sune jama’ar da suka rayu a karnin da nake). [Bukhari: 2652, Muslim: 2533] Wato Sahabbansa (RA).SIFFOFIN SAHABBAI (RA) DA ALLAH MADAUKAKIN SARKI YA BAYYANA A WANNAN AYAR:Dalilin da ya sanya Sahabbai da mabiyansu suka samu wannan yabo mai gwabi daga Ubangiji shine kasancewarsu:1) MASU UMARNI NE DA AIKATA ALHERI: Babban Umarni da aikata alheri shine umarni da Kadaita Allah da bautarsa shi kadai babu abokin tarayya, da kuma kiran jama’a zuwa addinin musulunci ta hanyar yada shi zuwa dukkanin sassa na duniya.(ZAN BADA ‘YAR GUNTUWARSURAR HAKAN DAGA BAYA).2) MASU HANI NE GA MUMMUNAN AIKI: Farkon abin da ya fi muni shine shirka, sannan kuma duk wani abu mummuna da shari’a ta yi hani a kansa.Al’ummun da suka gabata sun kasance sun yi sakaci sosai da wannan aikin mai girma, har Allah ya La’ance su, kamar yake cewa: (Sun kasance ba su hana junansu mummunan aikin da suka aikata. Hakika abin da suke aikatawa ya munana!). [Ma’idah: 79].Wadannan siffofi guda biyun farko (Umarni da abu mai kyau, da hani ga mummuna aiki) amfanuwar wasu ne, ba amfanin mai yinsu bane a asali, kenan Sahabban Ma’aiki sun samu kyakkyawartarbiya daga ma’aiki, wanda ya nuna musu cewa ka so wawaninka abin da kake so wa kanka, don haka domin wasunsu su amfana da shigacikin addinin musulunci, suma su samu wannan tsira da rabauta da su suka samu na yin Imani da Allah da ManzonSa – don hakan ne suka mike suka yi tsayuwar daka wajen isar da sakon Allah, da yada shi, tun Manzona duniya, har bayan wafatinsa (SAW).3). MASU IMANI NE DA ALLAH: su kansu sun siffantuta kamala, saboda sun yi Imani da Allah wanda shi yake basu damar aikata duk abin da Allah ya yi Umarni dashi, domin kuwa ba zaka kira wani zuwa hanyar tsira ba, sai kaima ka zama shiryayye. Wannan siffa kuwa raddi ne ga mushrikai, da suke bugar kirji kafin a bude Makka cewasune masu shayar da alhazai, kuma masu raya Masallacin Ka’ba, Allah yace:(Yanzu kun mayar da shayar da alhazai, da raya Masallaci mai alfarma kamar wanda yayi Imani da Allah da ranar lahira, kuma ya yi Jihadi saboda Allah? Ai ba za su taba zama daya ba a wurin Allah) [Taubah: 19].KADAN DAGA CIKIN JAN AIKIN DA SAHABBAI SUKA YINA YADA ADDINI BAYAN WAFATIN MA’AIKI (SAW):1- Manzon Allah (sallalLahu alaihi wa sallama) yana yin wafati, sai yawancin wadanda suka karbi musulunci a tsibirin larabawa suka yi ridda, bayan kuma Ma’aiki bai yi wafati ba sai da yawancin garuruwan tsibirin larabawa suka rissina suka mika wuya ga addinin musulunci. Abin da zai nuna hakan shine masu Sirah sun bayyana yawan wadanda suka yi hajjin ban kwana tare da shi da cewa adadinsu ya zarta mutum dubu dari.2- Farkon jan aikin da Abubakar Siddiq (RA) ya fuskanta shine: yakar ‘Yan ridda, Allah ya bashi nasarar ganin bayansu, kwarjinin addinin musulunci ya dawo. Bayan cikin gida ya gyaru, saiya juya waje, domin ci gaba da isar da sakon Ma’aiki SallalLahu alaihi wa sallama. Wanda tuni Ma’aiki SAW ya fara shimfidar hakan ta hanyar tura wasiku zuwa dukwani Sarki cikin sarakunan kafirci, yana kiransu zuwa addinin musulunci.Abubakar Siddiq (RA) ya kasarindinar musulunci kashi biyu: Kashi na daya suka doshi kasar Iraq a karkashin jagorancin Khalid bnil Waleed, sun samu nasarar bude kudancin Iraq a lokacin. Kashi na biyu kuma sun nufi kasar Sham da jagorancin Yazeed bn Abi Sufyan, da Shurahbeel bn Hasanah, da Mu’awiya, da Amru bnil As, sun samu nasarar bude Sham a yakin “Yarmuka” wanda ya faru a lokacin da Abubakar Siddiq (RA) shi kuma ya yi wafati.3- A zamanin Umar bnil Khattab (RA) [13 – 23 AH]:Mu’awiya (RA) ya yaki Rumawa, ya bude Jazeerah, da Armeniya, da Azrabeejan.‘Iyadh bn Ganam ya shiga gumurzun yaki har yakai (Bahr Qazween) (Wanda kogine da kasashe biyar a yanzu suke kewaye da shi: Russia, Iran, Azrabejan, Turkumanistan da Kazakhastan).Amru bnil As ya bude Misra, a lokacin har rundunar musulmai sun kai gefen kasar Libiya suka shiga Tripoli, da Barqah.A can Iraqi kuma Sa’d bn Abi Waqqas ya jagoranci bude garuruwan da suka ragu, bayan ya yi kaca-kaca da rundunar farisawa a yakin Qaadisiyyah, ya murkushe gaba dayan jagororinsu. Musulmai suka ci gaba da kutsawa iyakokin kasar Iran, suka bude Khurasaan, da Ahwaz, da yankin Farisa, suka kara nausawa kudanci har sai da suka kai Makran da kuma kan iyakar garin Sind (Pakestan). Suka kuma nausa gabas har sai da suka bude Sijistaan (Afganistan). (Wannan duk a zamanin Umar RA) kenan.Mu’awiya (RA) ya nemi izini daga Umar (RA) ya kutsa cikin kogi, don yakar wadanda garuruwansu suke haure, amma Umar ya hana saboda hadarin da yake tattare da hakan.4) A zamanin Halifa Usman bn Affan (RA) an kara bude Khurasan, da Armeniya, da Azrabejan saboda sun nuna kiriniya da bijirewa. A zamaninsa kuma a ka bude: Ray, da Hamzan, da Dabristaan, da Jurjan, aka karasa bude gaba dayan Iran. Aka halaka sarki na daular Farisa wato Yazdajirdu bayan ya karade duniya yana ta guje-guje.A can Sham kuwa ‘yan garuruwa ne kadan suka ragu wadanda suke karkashin daular Rumawa suma Mu’awiya (RA) ya karasa bude su.A zamanin Usman (RA) har wayau ya bayar da izinin a kutsa ta kan kogi don yin Jihadi, ba tare da bata lokaci ba, sai Mu’awiya (RA) ya sanya tsarin rindina kashi biyu: Masu Jihadi a lokacin Zafi, da Masu Jihadi a lokacinsanyi, ya yi wannan tsarin ne don a ci gaba da yakar Rumawa ba yankewa. A shekara ta (27 Ah) ya samu nasara a kan Rumawa har saida ya isa kasar Qustantinia = Constantinople (Istanbul) ya kewayeta.A garin Akka da take hannun Israel a yanzu Mu’awiya ya gina ma’aikatar kera Jiragen ruwan yaki (Naval fleet), kuma aka ci nasarar kera babban jirgin ruwan yaki na farko a musulunci, manufarsa itace kutsawa kasashen turawa kamar su Cyprus da take kudu maso gabashin turai, da Arwaad datake kusa da garin (Tarsus) tacikin Syria.A Misra kuma rindinar musulunci ta ci gaba da nausawa yamma, tana kutsawa kasashen Afrika, karkashin jagorancin Abdullahi bn Sa’d bn Abi Sarh, inda ya karya rindinar Rumawa da jagorancin (Gregorius), ya bude garuruwa arewacin Africa har ya dangana da garuruwan kasar Moroco.5). A lokacin Aliyu bn Abi Talib (RA) saboda fitina da ta kunno kai a garuruwan musulmai, ba a samu an ci gaba da bude-bude ba, tun da sai gida ya gyaru sannan za’a gyara waje.WADANNAN BUDE-BUDEN DUK ANSU SAHABBAN MA’AIKI NE SUKA JAGORANCE SU KUMA DUKA-DUKA AN YI SUNE A CIKIN SHEKARU 25 KACAL. WADANNE IRIN MUTANE NE ZASU IYA KWATANTA IRIN WANNAN MURGUJEJEN AIKIN? KUMA IDAN AN BUDEGARI FA, BA WAI SHIKE NAN BA, A’A AKWAI MALAMAI A CIKIN SAHABBAI DA AKE TURA SU GARURUWA, SU KUMA AIKINSU SHINE SU KARANTAR DA MUTANEN GARIN AL’AMURAN ADDININMUSULUNCI. MAYAKA NE, KUMA MALAMAI NE; TA HAKA ADDININ MUSULUNCI YA YI YADUWAR DA BAI TABA IRINTA BA.LALLAI ALLAH YA YI GASKIYA:(Kun kasance al’uma mafi alheri da aka fitar wa mutane: kuna umarni da [aikata] alheri, kuma kuna hani ga mummunan aiki, kuma kuna yin Imani da Allah). [Aal Imran: 110].Allah ya saka musu da alheri,ya kara yarda a gare su, ya bamu ikon yin koyi da koyarwarsu, ya hada fuskokimmu tare da su a aljanna. Ameen Ya rabbal ‘Alameen.

Reply

nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

ADDININ GASKIYA (4)

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:33 PM

ADDININ GASKIYA (4)SAHABBAN MA’AIKI (SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAMA) DA ALAYENSAAlhamdu lilLah, Wassalatu Was-Salamu ‘ala RasulilLah, wa ‘ala alihi wa sahbihi wa man tabi’ahum bi ihsaanin Ila yaumid deen.Har yanzu dai muna kan bayanin ayoyin da Allah Madaukaki ya yi yabo da kirari ga jimillar Sahabban Ma’aiki (SAW) ba tare da ware wasu sinfi ba.Allah Madaukakin Sarki yana cewa:( ﻻ ﻳﺴﺘﻮﻱ ﻣﻨﻜﻢ ﻣﻦ ﺃﻧﻔﻖ ﻣﻦ ﻗﺒﻞ ﺍﻟﻔﺘﺢ ﻭﻗﺎﺗﻞ، ﺃﻭﻟﺌﻚ ﺃﻋﻈﻢ ﺩﺭﺟﺔ ﻣﻦ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺃﻧﻔﻘﻮﺍ ﻣﻦ ﺑﻌﺪُ ﻭﻗﺎﺗﻠﻮﺍ ﻭﻛﻼًّ ﻭﻋﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺤﺴﻨﻰ ( ﺍﻟﺤﺪﻳﺪ: 10(Wanda ya ciyar daga cikinkutun kafin bude [Makka] ya kuma yi yaki ba zai zama daidai ba [da wanda ya ciyar daga baya ya kuma yi yaki, wadancan sun fi daraja fiye da wadanda suka ciyar bayanbude (Makka) suka kuma yi yaki, amma kuma gabadayansu Allah Ya yi musu alkawarin kyakkyawan sakamako [na shiga Aljanna]). [Hadid: 10].Allah Madaukaki ya bi salo daban-daban wajen bayyana girman darajar Sahabban Manzon Allah (SAW), ban da wannan ayar da muke bayania kanta, akwai inda ya nuna cewa wasu daga cikin Sahabbai sun fi wasu girmandaraja, ya bayyana cewa wadanda suke jihadi sun fi wadanda suke zaman gida batare da wani uzuri ba daraja. Amma kuma gaba dayansu, Allah ya yi musu alkawarin “kyakkyawan sakamako” wato Aljanna. [Duba Suratun Nisa': 95].Su kuwa masu uzuri suna da irin ladan wadanda suka fita jihadi, saboda Allah ya ga zuciyoyinsu, kamar yadda Anas (RA) ya karbo daga Ma’aiki (SAW) a lokacin da yake komowa daga yakin Tabuka yana cewa:(Hakika akwai wasu mutane da suke cikin Madina, duk wata tafiya da kuka yi, duk wani kwari da kuka tsallake suna tare da ku). Sahabbai suka yi mamaki sukace: Ya Ma’aikin Allah! Kuma bayan suna can zaune a cikin Madina? Sai yace: (I, suna da uzurin da ya hana su fitowa tare da ku). [Bukhari: 4423].A Ayar (Suratun Nisa’) An bayyana falalar masu Jihadi gaba dayansu, kuma gaba dayansu Allah ya yi musu alkawarin (Husna = Aljanna).A Ayar da muke bayaninta kuma an bayyana cewa sumamasu jihadin hawa-hawa ne:1). Masu kololuwar daraja, da suke kan gaba wajen girman matsayi a wurin AllahMadaukakin Sarki. (Sune wadanda suka ciyar da dukiyoyinsu, suka yi jihadi kafin budi).2). Wadanda suke biye dasu a daraja da girman matsayi awurin Allah (Sune wadanda suka ciyar da dukiyoyinsu, suka yi jihadi bayan budi).Malaman Tafsiri sun kari juna ilimi a kan ma’anar “Budi” da aka ambata a wanann ayar:a). Jamhurinsu sun rinjayar da cewa abin da ake nufi da “Budi” a wannan ayar shine: Bude garin Makkah, wanda aka yi a shekara ta takwas (8) bayan hijirar Ma’aiki (SAW).b). Wasu kadan daga cikinsu kuma suka ce abin nufi da “Budi” shine: Sulhun Hudaibiyah, wanda aka yi shia shekara ta shida (6) bayan hijira. Sun ce saboda shine ya share hanyar kasantuwar Makka a hannun musulmi, kuma Allah ya kira shi “budi” a Suratul Fat’h.AMMA MAGANAR FARKO ITATAFI RINJAYEN DALILI. WATOMA’ANAR ‘FAT’H’ SHINE ‘FATHU MAKKA’ DA AKA YI A SHEKARA TA (8).Wannan Ayar ta bayyana girman falalar Sahabban farko, wadanda suka taimakawa Ma’aiki a lokacin da addini yake cikin tsananin bukatar mai taimako, sun taimaka da sayar da rayukansu, sun ciyar da dukiyoyinsu, a lokacin da babu jama’a da yawa tare da Ma’aiki, ga karfi da yawan adadi da arna kafurai suke da shi, amma suka bi Ma’aiki,basu girgiza ba, ba su raurawa ba. Babu shakka wadannan Sahabban sun fi girman daraja da falala a kanwadanda suka musulunta lokacin da musulunci ya yi karfi, kafurci ya yi kasa, ya yi rauni. Shi ya sanya Allah ya yabi Sahabban farko a ayoyi da yawa a cikin Kur’ani.Amma gaba dayansu Allah ya yi musu alkawarin Aljannaﻭَﻛُﻼًّ ﻭَﻋَﺪَ ﺍﻟﻠﻪُ ﺍﻟْﺤُﺴْﻨَﻰ .SIFFOFIN SAHABBAN MA’AIKI (SAW) A WANNAN AYA:1). CIYARWA A LOKACIN RINTSI DA KUMA YALWA: Wasu daga cikinsu suna da dukiya mai yawa, don haka suna ciyar da dukiyoyinsu wajen yada addini. Kamar yadda Usman bn Affan (RA) alokacin da ake kawo gudummawa don shirya rindinar da zata tafi yakin Tabuka, ya kawo Dinare Dubu wajen Ma’aiki (SAW) a matsayin gudummawarsa, Ma’aiki ya rika juya dukiyar, don tsananin mamakin girman irin wannan gudummawar har ya rika cewa: (Daga yau [saboda girman lada], ko me Usman zai aikata ba zai cuci girman aikin nan nasa ba!). Ma’aiki (SAW) ya yi ta fadin hakan yana kara maimaitawa. [Tirmizi: 3701, Hakim: 3/110].Wasu daga cikin Sahabbai wadanda ba su da halin tallafawa, amma don su rabauta da gaggwaban ladanciyarwa sai suka rika yin aikin karfi cikin rana, suna yin dako, suka kawo dan abinda suka iya samowa a matsayin gudummawarsu, kamar yadda Abu Aqeel (Wani sahabi) ya yi, har ya samu ya hada Sa’i guda (wato Mudunnabi hudu ko biyar) na abinci, shima ya bayar a matsayin gudummawa.Su kuwa munafukai basu kyale kowa ba, ba wanda ba su yi zundensa ba: su rika cewa wadanda suka iya kawodukiya da yawa: “Ai riya ce kawai! Wai don a ce ya burge!”. Wadanda kuma sukakawo kadan bayan jibin goshida aikin karfi, sai suka rika cewa: “Yo me Allah zai yi da dan wannan abin da kuka kawo! Abin kunya kawai!”.Don haka aya ta sauka tana kare Sahabban Ma’aiki (SAW)daga cutarwar da munafukai suka rika yi musu a wannan lokaci. [Duba Bukhari: 4668].(Idan mun tashi yin bayanin siffofin munafukai, da yadda suka yi hannun riga da hanyar Sahabbai za mu yi karin bayani In sha’Allah).Amma dai abu mai mahimmanci a nan shine siffantuwar Sahabbai da siffata ciyarwa.2). Fita Jihadi: Wannan kuwa ba sai an yi dogon bayani ba,yadda Sahabbai suke kwadayin halartar duk wasu yake-yake da ake yi, babu gudu, ba ja da baya, wasu ma har kuka suka rika yi, suna cizon yatsa saboda yaki ya tsere musu.Kamar yadda Anas bn Nadhr(RA) aka yi rashin dace ba ya gari lokacin da aka fita yakin Badar, kafin kuma ya dawo har an yi yaki an gama, sai yarika cewa:(Wallahi idan dai har Allah yanuna min wani yakin a nan gaba, Allah zai ga abin da zanyi!) don haka ranar Uhud suna gaba-gaba wajen fita don karawa da arna, ya shigagumurzu har aka kashe shi, lokacin da aka kare yakin, aka same shi cikin wadanda suka yi shahada, an lissafa sara, da suka, da harbi a wurare fiye da tamanin a jikinsa, gashi an yanke wasu sassan jikinsa. Jama’a suka kasa shaida ko wanene, sai ‘yar uwarsa ce ta iya shaida shi, ita ma da ‘yan yatsun hannunsa ta iya gane shi. [Bukhari: 2805].Allah Madaukaki yana cewa:( ﺇﻥ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺳﺒﻘﺖ ﻟﻬﻢ ﻣﻨﺎ ﺍﻟﺤﺴﻨﻰ ﺃﻭﻟﺌﻚ ﻋﻨﻬﺎ ﻣﺒﻌﺪﻭﻥ (…ﺍﻷﻧﺒﻴﺎﺀ، ﺍﻵﻳﺎﺕ: 113-111(Hakika wadanda albishir ya zo musu daga gare Mu su wadannan nesanta su ake yi daga gare ta [wutar]. Ba su jin hargowarta, kuma su masu dawwama ne cikin abin da ransu yake so. Babbar firgita [wannan ranar] ba ta samun su, kumaMala’iku za su tare su [suna cewa] Wannan ita ce ranar taku wadda kuka aka yi mukualkawarinta [a duniya]). [Anbiya': 111-113].Fadakarwa: A baya mun yi bayanin yawan rundunar da Ma’aiki ya fita Bude Makka da ita, yawanta ya kai 10,000.Don haka a yadda akasarin malamai suka tafi na cewa abin nufi da “budi” a ayar da muka yi bayaninta shine bude Makka, zamu iya suranta yawan wadanda suka shiga jerin masu kololuwar daraja a wajen Allah, kuma Allah ya yi musu alkawarin Aljanna, Allah ba ya saba alkawari, kuma ba yacanza magana (Tsarki ya tabbata a gare shi!).Masu bakin ciki da ciwon zuciya kuwa suna ganin wannan hukuncin da Allah yayi ba daidai bane, wadanda zasu shiga Aljannar a wajensu basu fi a kirge su a tafukan hannu biyu ba. To saimu gani ko Aljannar a hannunsu take!A baya na yi bayanin kadan daga cikin ayoyin Kur’ani da suka yi yabo da kirari ga jimillar Sahabban Ma’aiki (SAW) Allah ya kara musu yarda. Ga dukkan wanda ya yi duba da idon basira cikin wadannan ayoyin, zai fahimciirin girman falala da darajar da Sahabbai suke da ita a wajen Mahaliccin kowa da komai, don haka babu wani kuma mai tsaurin ido da rashin lafiyar zuciya, da tsatsarta da ya isa ya kawo wani abu sabanin hakan, har kuma a samu mutum musulmi mai takama da musuluncinsa ya tsaya yana sauraron wani marili, mai nakasassheyar kwakwalwa da baudewarta. Babu shi, ba’a yi shi ba, kuma ba za’a yishi ba.A yanzu zan takaitu da wadannan ayoyin a wannan kashin, don haka zan shiga kashi na gaba, wanda ya kunshi wasu jerin ayoyi da suke karin yabo da kirari ga wasu sinfi na musamman cikin Sahabbi, wato: Muhajirun da Ansar (Allah yakara musu yarda):KASHI NA BIYU: YABO DA KIRARI DAGA ALLAH MADAUKAKIN SARKI GA SAHABBAN MA’AIKI (SAW) = MUHAJIRUN DA KUMA ANSAR:Kafin bayanin wadannan ayoyi, zai yi kyau matuka na yi karin haske game da wadannan jama’a, domin kuwa duk wani musulmi da zai buda Littafin Allah lallai zai ta cin karo da dimbin ayoyin da Allah ya yi ta ambaton alheransu da daukakar darajarsu, da hasken falalarsu a wurare daban-daban, da kuma salo iri-iri:MUHAJIRUN: Siffar “Muhajir”ta samo asali ne daga kalmar“HIJRAH” wadda a harshen hausa take nufin KAURA. Su kuwa Muhajirun an basu wannan siffa ne saboda sun kauracewa gidajensu, da masaukansu; suka kyamaci zama tare da kafurai, ko kuma zamowa karkashin mulkinsu, saboda ba su aminta daga fitinarsu ba. Suka kaurace musu zuwa inda suka samu aminci da nutsuwa. Kamar yadda Muminan farko (Sahabbai) suka kauracewa garin Makka zuwa birnin Madina. [Tafsirud’ Dabri: 4/318]A yaren shari’a idan aka ce: Muhajirun, to kai tsaye ana nufin Sahabban Ma’aiki SAW wadanda suka yi kaura daga Makka zuwa Madina don su gudu da addininsu daga fadawa cikin fitinar kafurai da kafurci. Hijira Sunna ce ta Annabawan da mutanensu suka saba musu a addini, Annabi Ibrahim ya kauracewa mutanensa, yace: (Ni mai yin hijira ne zuwa ga Ubangijina) [Ankabut: 26].Annabi Lud shima ya yi hijira. Annabi Musa ma ya fita daga kasar Misra tare da mutanensa don tsere wa fitina da kiriniya ta Fir’auna. Annabi Muhammad (SAW) tare da Sahabbansa suma sun yi hijira zuwa garin Madina, kafin nan kuma ya yiwa Sahabbansa izinin yin hijira zuwa kasar Habasha. [At Tahreer wat Tanweer: 10/84].Hijirar da Ma’aiki (SAW) ya yi ta zuwa Madina tare da Sahabbansa sifface babba data cancanci tarin yabo; don haka ne ma Ma’aiki SAW yakebayyana ta a matsayin falala mai matukar girma, inda yake rarranshin Ansarawa yake cewa a hadisin da Abdullahi bn Zaid bn Asim RA ya karbo:(Ba don dinbin falalar da take cikin hijira ba, da ni ma na zamo daya daga cikin Ansarawa (mutanen Madina)[Bukhari: 4330].Sahabi ba ya cin wannan siffa ta “Muhajir” har sai idanhijirar tasa da ya yi ta zuwa Madina (Birnin Manzon AllahSAW) ta auku kafin bude garin Makka a shekara ta takwas (8) da hijirar Manzon Allah (SAW).Dalilin hakan kuwa shine Hadisin da Ibnu Abbas (RA) ya ruwaito daga Manzon Allah (SAW) yace:(Babu sauran hijira [zuwa Madina da za’a baiwa mutumladansa] bayan an riga an bude garin Makka, abin da dai ya yi saura shine: Jihadi, da kuma ladan niyya). [Bukhari: 2783, Muslim: 1353].Wannan shine bayani takaitacce game da “MUHAJIRUN”.ANSAR: Sahabbai Mutan Madina, wadanda suke daga kabilun Aus da Khazraj. Sun ci wannan siffar tasu ce wadda ginshikinta yake daga kalmar “NASR”, ita kuwa tananufin TAIMAKO.Sahabbai mutanen Madina sun taimaka wajen yada addinin Allah, da kuma bashikariya ta hanyar bayar da masaukai ga musulmai a garinsu, da gidajensu, da kum ciyar da dukiyoyinsu don Allah. Taimakon da suka yi wa addinin musulunci ya faru ne tun kafin a bayar da izinin yin jihadi, sun taimakawa Ma’aiki (SAW), sun dauki alwashin zasu bashi kariya da shi da sauranmusulman da suka iso garin nasu (Madina), kamar yadda zasu baiwa iyalansu kariya.Manzon Allah (SAW) yana matukar kaunar Ansarawa, yana girmama su, yana bayyana falalarsu, kamar yadda muka gani a hadisin da ya gabata.Mafi ban sha’awa ma shine ya rokar musu gafarar Allah, da Su, da ‘ya’yansu, har ma da jikokinsu, kamar yadda yazo a hadisin Anas bn Malik (RA) yace:(Jigilar debo ruwa bisa taguwa don baiwa shukoki yatsananta ga Ansarawa mutanen Madina, sai suka shirya zuwa wurin Ma’aiki (SAW) don su roki ya yi musuaddu’ar samun sauki, ko kuma ya sa a ha’ka musu magudanar ruwa da zata taimaka musu. Sai labarin abin da suka nufa ya kai kunnen Annabi (SAW), shi kuma kafin zuwansu yace: “Duk abin da kuwa [Ansarawa] suka roka a yau to [Allah] zai amsa musu”. Sai suma suka samu labarin wannan maganar da [Ma’aiki ya yi kafin su je], da suka ji haka, sai suka roki Ma’aiki (SAW) da ya rokar musu Allah ya gafarta musu. Sai Ma’aiki (SAW) yace: “Ya Allah,ka gafarta wa Ansarawa![Ya Allah ka gafartawa] ‘ya’yansu! [Ya Allah ka gafartawa] ‘ya’yan ‘ya’yansu! [wato jikokinsu]. [Ahmad: 13226 da isnadi mai inganci].Daga cikin ayoyin da suka nuna girman wadannan Sahabban (Muhajirun da Ansar) akwai fadin Allah madaukakin Sarki:( ﻭﺍﻟﺬﻳﻦ ﺁﻣﻨﻮﺍ ﻭﻫﺎﺟﺮﻭﺍ ﻭﺟﺎﻫﺪﻭﺍ ﻓﻲ ﺳﺒﻴﻞ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﺬﻳﻦ ﺁﻭﻭﺍ ﻭﻧﺼﺮﻭﺍ ﺃﻭﻟﺌﻚ ﻫﻢ ﺍﻟﻤﺆﻣﻨﻮﻥ ﺣﻘﺎًّ،ﻟﻬﻢ ﻣﻐﻔﺮﺓ ﻭﺭﺯﻕ ﻛﺮﻳﻢ ( . ﺍﻷﻧﻔﺎﻝ 74:(Wadanda kuma suka yi Imani, kuma suka yi hijira, suka kuma yi yaki saboda Allah, da wadanda kuma suka sauki [masu hijira] sukakuma taimaka, wadancan sune muminai na hakika. Suna da [sakamakon] gafara da kuma arziki mai girma). [Anfal: 74].Amma zan takaita a nan, wani jikon in Allah ya yarda zan yi sharhi madaidaici game da wannan ayar, na yi karin haske dangane da irin girman kirari da bayanin falalar Sahabbai da ta kunsa.Amma kafin na rufe magana ta, tun da yau mun yi tsokaci kadan game da Muhajirun daAnsar, yanzu ga wata tambaya a matsayin KACICI-KACICI, da fatanmasu karatu zasu canko:AKWAI SAHABBAI GUDA HUDU DA SUKA CI SIFFOFI GUDA BIYU: MUHAJIRUN NE,KUMA ANSAR NE, SU WANENE WAADANNAN SAHABBAI GUDA HUDUN?WANDA YA AMSA ZA MU YI MASA FATAN ALLAH YA SAKA MASA DA MAFIFICIN ALHERANSA?

Reply

nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

mu awuya 2

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:26 PM

SHIN KASANCEWA SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN ALJANNANE ??.KASHI NA BIYU.ﻭﺻﻼﺓ ﻭﺳﻠﻢ ﻋﻠﻰ ﺧﻴﺮﺧﻠﻖ > ﻣﺤﻤﺪ ﺹ < ﻭﻋﻠﻰ ﺍﻟﻪ ﻭﺃﺻﺤﺒﻪ ﺍﺟﻤﻌﻴﻦ .ACIGABAN KARATUN MU WANDA KE NUNI DA KASANTUWAR SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN GIDAN S.HINDU DAGA S.ABU SUFIYAN {RD}.KASHI NA BIYU.YAU ZAMU DORA BADAN KOMAI BA.SAI DAN NASIHA GA YAN UWA MASU ILIMI DA HANKALI WAJEN SUGUJI FADAWA IRIN WANGA MASIFA TA ZAGIN MASU HIDIMA GA MA,AIKI { S.A.W } SHAIDA TAFARKO DAGA MANZON ALLAH S.A.W. YANA CEWA.ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻋﻠﻢ ﻣﻌﺎﻭﻳﺔ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺤﺴﺎﺏ ﻭﻗﻪ ﺍﻟﻌﺬﺍﺏ . >ﺍﺣﻤﺪ ٤ /١٢٧ ﻭ ﻓﻀﺎﺋﻞ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ١٧٤٨ ﻭﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻓﻲﺍﻟﻜﺒﻴﺮ ١٨ /٦٢٨ ﻭﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ﻓﻲ ﺗﺎﺭﻳﺨﻪ ٧ /٣٢٦ ﻭﺍﺑﻦ ﺧﺰﻳﻤﺔ١٩٣٨ ﻭﺍﻟﻬﻴﺜﻤﻲ ٩ /٣٥٦ ﻭﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺹ ٣٢٢٧ .TO MA,AIKI GASHI DAKANSA YANA NEMAN ALLAH DA YASANAR DA SAYYIDUNA MU,AWUYYA ILIMINALQUR,ANI DA KUMA IYA LISSAFI.KUMA YATSARESHI AZABAR WUTA.KAGA KUMA WALLAHI ALLAH YA,ANSHI WANGA ROQO NA MA,AIKI.KAGA INMUKAJIKA KANACEWA SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN WUTANE TO BADAMU KAKEJAYAYYA BA DA MA,AIKIKAKE.INKA KASANCE MAI QAUNA GA MA,AIKI TO KAME ABIN SALATINKA .TO GAKUMA WATA SHEDAR DAGA WAJEN ALLAH.ﻓﻲ ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﺤﺪﻳﺪ ﺍﻳﺔ ١٠ -ﻻﻳﺴﺘﻮﻱ ﻣﻨﻜﻢ ﻣﻦ ﺍﻧﻔﻖ ﻣﻦ ﻗﺒﻞ ﺍﻟﻔﺘﺢ ﻭﻗﺘﻞ ﺍﻭﻟﺌﻚ ﺍﻋﻈﻢ ﺩﺭﺟﺔ ﻣﻦ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺍﻧﻔﻘﻮﺍ ﻣﻦ ﺑﻌﺪ ﻭﻗﺘﻠﻮ ﻭﻛﻼ ﻭﻋﺪﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺤﺴﻨﻰ ....ALLAH YANA GAYAWA SAHABBAI CEWAR BAZASU TABA ZAMA DAIDAI BA DAWADANDA SUKACIYAR KAFIN FATAHU MAKKAH KUMA SUKAYI JIHADI,WADANCHAN SUNE MAFIDARAJA AKAN WADANDA SAI BAYAN FATAHU MAKKAH SUKAYI JIHADI DA KUMA CIYARWA, TO AMMA DUKKANSU ALLAH YAYIMUSUTANADI MAI KYAU ﻭﻗﺎﻝ ﻣﺠﺎﻫﺪ ﻭﻗﺘﺎﺩﺓ >ﺍﻟﺤﺴﻨﻰ .:ﺍﻟﺠﻨﺔ <. ﺗﻔﺴﻴﺮ ﺍﺑﻦﺟﺮﻳﺮ ٢٧ /١٢٨ ﻭﺍﺳﺘﺪﻝ ﺍﺑﻦ ﺣﺰﻡ ﻣﻦ ﻫﺬﻩ ﺍﻻﻳﺔ ﺑﺎﻟﻘﻄﻊﺑﺄﻥ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ﺟﻤﻴﻌﺎ ﻣﻦ ﺍﻫﻞ ﺍﻟﺠﻨﺔ }ﺍﻟﻔﺼﻞ ٤ /١٤٨ - ١٤٩ }MALAN MUJAHID DA QATADA DA IBN HAZIM DUKANSU SUNKAFA HUJJA DA WANGA AYAR AMATSAYIN DALILI AKANCEWAR DUKKAN SAHABBAI YAN ALJANNA NE..TO KUMA YATABBATA SAYYIDUNA MU,AWUYYA YABAYYANA MUSULUNCINSA NE A ASHEKARAR BUDE MAKKAH{ ﺗﺎﺭﻳﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﻟﻠﺬﻫﺒﻲ _ﻋﻬﺪ ﻣﻌﺎﻭﻳﺔ٣٠٨ }TO KAGA KENAN YANA DAYA DAGA CIKINWADANDA ALLAH YAYI MUSU TANADI NAALJANNAH.KUMA MASUCEWA SAYYIDUNA MU,AWUYYA KAFIRI NE KO MUNAFUKI NEKO FASIQINE TO DA ALLAH SUKE RIGIMA.DAN ALLAH YANA FADA CIKIN.ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﺤﺠﺮﺓ ﺍﻳﺔ ٧ .ﻭﻟﻜﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﺣﺒﺐ ﺇﻟﻴﻜﻢ ﺍﻷﻳﻤﻦ ﻭﺯﻳﻨﻪ ﻓﻲ ﻗﻠﻮ ﺑﻜﻢﻭﻛﺮﻩ ﺇﻟﻴﻜﻢ ﺍﻟﻜﻔﺮ ﻭﺍﻟﻔﺴﻮﻕ ﻭﺍﻟﻌﺼﻴﺎﻥ ﺍﻭ ﻟﺌﻚ ﻫﻢ ﺍﻟﺮﺍﺷﺪﻭﻥ .KAGA ALLAH YANACEWA YASANYA MUSU QAUNAR IMANI KUMA YAQAWATA MUSUSHI AZUKATANSU YAKUMA SANYA MUSU QIN KAFIRCI DA FASIQANCI DA SABAMASA .KUMAYACE SUNE SHIRYAYU.KAI KUMA KANA BAHAKA BA TO DA SHI KAKE RIGIMA.ZAMU CIGA BA.

Reply

nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

mu awuya 1

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:26 PM

SHIN KASAN CEWA SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN ALJANNA NE ?.KASHI NA DAYAﻭﺻﻼﺓ ﻭﺳﻠﻢ ﻋﻠﻰ ﺭﺳﻮﻝ ﻟﻠﻪ .HAQIQA SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN GIDAN ABU SUFIYAN DA GA S.HINDU DAN ALJANNA NE .KUMA BISA DALILI NA AYA DA HADISI.KAFIN IN,FARA ZANYI WANI DAN TANBIHI AKAN WANGA KALMAﺍﻟﺼﺤﺎﺑﻲSABODA NAGA WASU BASU SAN MAI AKENUFI DA ITA BA.TO HAQIQA MALAMIN MUSULUNCI ALITTAFINSA YA BAMUBAYANIﻫﻮ ﻣﻦ ﻟﻘﻲ ﺍﻟﻨﺒﻲ >ﺹ <ﻣﺆﻣﻨﺎﺑﻪﻭﻣﺎﺕ ﻋﻠﻰ ﺍﻹﺳﻼﻡ . } ﺍﻹﺻﺎﺑﺔ 1/10 }KAGA KENAN S.MU,AWUYYA YANA CIKI.TO BARI MUJI MAI ALLAH YACE AKANSU MU,AWUYYA ﻓﻲ ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﺘﻮﺑﺔ٨٩، ٨٨ﻟﻜﻦ ﺍﻟﺮﺳﻮﻝ ﻭﺍﻟﺬﻳﻦ ﺀﺍﻣﻨﻮﺍ ﻣﻌﻪ ﺟﻬﺪﻭﺑﺄﻣﻮﺍﻟﻬﻢ ﻭﺃﻧﻔﺴﻬﻢ ﻭﺃﻭﻟﺌﻚ ﻟﻬﻢ ﺍﻟﺨﻴﺮﺍﺕ ﻭﺍﻭ ﻟﺌﻚ ﻫﻢ ﺍﻟﻤﻔﻠﺤﻮﻥ .ﺍﻋﺪﺍﻟﻞﻩ ﻟﻬﻢ ﺟﻨﺖ ﺗﺠﺮﻱ ﻣﻦ ﺗﺤﺘﺤﺎ ﺍﻷﻧﻬﺮ ﺧﻠﺪﻳﻦ ﻓﻴﺤﺎ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻔﻮﺯﺍﻟﻌﻈﻴﻢ .TO ALLAH YANACEWA SAI DAI CEWARMANZONSA TARE DAWADAN DA SUKAYI IMANI DA SHI KUMA SUKAYI JIHADI DA DUKIYOYINSU DA KAWUNANSU TO HAQIQA SUNA DAALKHAIRI KUMA HAQIQA SUNE MASU RABAUTA KUMA ALLAH YAYI MUSU TANADI NA ALJANNAH WACCE QORAMAI KE GUDANA ACIKINTA KUMA SUNA MASUDAWWAMAACIKINTA WANNAN SHINE RABO MAI GIRMA.TO TABBASA SAYYIDUNA MU,AWUYYA YANA DAYA DAGA CIKIN WADANNAN MUTANE. KAGA KENAN DAN ALJANNA NEDA FADIN ALLAH KUMA GA SHI MA,AIKI YANA FADA CIKINﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ٢٩٢ ﻭﺍﻟﺒﺪﺍﻳﺔ ٥ /٦٢٩ﻗﺎﻝ > ﺹ < ﺃﻭﻝ ﺟﻴﺶ ﻣﻦ ﺃﻣﺘﻲ ﻳﻐﺰﻭﻥ ﺍﻟﺒﺤﺮ ﻗﺪ ﺍﻭ ﺟﺒﻮﺍ ﻭﺍﻭﻝ ﺟﻴﺶ ﻣﻦ ﺍﻣﺘﻲ ﻳﻐﺰﻭﻥ ﻣﺪﻳﻨﺔ ﻗﻴﺼﺮ ﻣﻐﻔﻮﺭﻟﻬﻢ .ﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﺤﺠﺮ : ﺍ ﻗﺪ ﺍﻭﺟﺒﻮ ﺍﻱ ﻓﻌﻠﻮﺍ ﻓﻌﻼ ﻭﺟﺒﺖ ﻟﻬﻢ ﺑﻪ ﺍﻟﺠﻨﺔ .١٠٣MA,AIKI YACE FARKON RUNDUNAR DAZATA FARA YAQI TACIKIN KOGI TO HAQIQA TAWAJABA AGARE SU < ALJANNAH > KUMA FARKON RUNDUNAR DATA YAQI GARINQAISARA TO ANGAFARTA MUSU.TO KUMA WADANNAN YAQIN HARDAMU,AWUYYA ZAKA IYA KOMAWAFATAHULBARIY KAGANI.SHIN KASAN ANNABI YASAN ZASUYI RIKICI SHI DA SU SAYYIDUNA ALIYU DA SAYYIDUNA AMMAR AMMA KUMAYACE ZASU SHIGA ALJANNAH KUMA KOMAI ZASUYI ANGAFARTA MUSU ?TO SHIN BAKA BIYAYYANE GA MA,AIKI ?TO HAR,INDAI KANA BIYAYYA TO CENE MUSU YAN,ALJANNA KUMA WADANDA AKA GAFARTAWA.IDAN KUMA KAKARANTA TARIHI NE KO WANI ABU KAGA LAIFIN WANI TO KATUNAFA ANGA FARTAMUSU.KO KUMA KAKAME BAKIN KA KAMARYAN DA YAYI UMARNI.ZAMUCI GABA

Reply

nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

HISTORY OF ISLAMIC THEOLOGY (bI)

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:14 PM

4. Debates like this – if there is any need of it – should be between experts from both sides in a separate forum, that is on private e-mail addresses, the result ofwhich will later be made known to the NMN and its members. And the medium of communication should strictly be the language in which original Islamic books arewritten, that is the arabic language, to avoid misapprehensions that reallyoccur in translations.5. Brothers should not wastetheir talents debating upon some topics selected by the Shi’ites intentionally to createan amount of doubt in the minds of muslims asregards their sources. For one thing many do not observe is that Shi’ite attacks on the Sunnis is mostly – if not always – on either the authenticity of the Qur’an,that is by reminding you that this Qur’an was collected andwritten in the final form of a book in the time of the first caliphs, Abubakar, Umar andespecially inthe reign of Uthman in whichit was compiled and distributed to all muslim countries – or the authenticity of the Sunnah and that is by making you believe that theSahaba through whom we received the whole of this religion are infidels, not trustworthy etc., the result ofwhich is either a total negation of anything narratedby them or at least doubting its authenticity. This I will discuss in more detail- in shaAllah – under the topic of theShi’ites stand on the Sahaba, and their conceptof ‘ismah (infallibility) of the Imams.6. The best thing therefore is for the muslim ummah to know who these people are, what they carry with them asreligion, where they are heading to, what theircreeds and beliefs are built on, who their predecessors are after alienating the companions of the prophet e, are they true lovers of the Ahl-Bayt etc.Thus by virtue of my specialisation, I have a humble contribution to makein this field, in the form of objective and fair research. I had done a detailed researchon the various sects in Islam and their historical origins, both existing and those that have died out with the passage of time, and I was intending to present a briefsummary of this research to my fellow brothers in this forum, when the issue of Shi’ism came up. Thus I havedecided to start by giving a detailed discussion onShi’ah right from the time of its conception and delivery up to its present day manifestation, in an objective and scholarly manner, vowing not to mention anythingbelieved by the Shi’ites but from their authentic books generally accepted and recognized by their mullahs. Later on, in sha Allah, I can go back to other parts ofthe topic in a series of articles. This, I believe, will be more useful to members who really want to know.**NOTEThis is a series of artices written by the Sheikh, as a sincere reminder to the (Nigeria Muslim Forum) way back in 2008.

Reply

nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

HISTORY OF ISLAMIC THEOLOGY (I)

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:04 PM

Bismillahir Rahmanir RahimAll praise is due to Allah, we praise Him and seek His assistance and guidance. We repent unto Him and seek His protection against the evils of our souls and that ofour bad deeds. Whomever Allah guides none can mislead, and whomsoever He misleads none can guide. I bear witness that there is none worthy of being worshipedexcept Allah, alone without partner, and I bear witness that Muhammad is His servant and messenger. MayAllah’s peace and blessings be bestowed upon him and hispure family and noble companions.((O ye who believe, fear Allahas He ought to be feared anddie not except as Muslims))((O mankind fear your Lord who created you from a single soul, and from it its mate and from the two of them scattered many males and females, fear Allah inwhose Name you beg one another, and (be mindful of) your kinship, most certainly Allah keeps a watch over you)).((O ye who believe, fear Allahand say that which is straight(and true), He will correct, for you, your deeds and forgive your sins, whoever obeys Allah and Hismessenger has certainly succeeded a great success)).As a new member of this forum, I have taken time observing the different write-ups from fellow brothers in the NMN, and was waiting for the time it will be ripeto start writing on issues thatwill be of benefit to all – bothreligiously and in their various fields of endeavour, issues that no muslim living today can afford tobe ignorant of, if he really wants to succeed in life and his role as a vicegerent of Allah on earth; and issues which unfortunately nobody seems to be turningattention to, much-less writing about.Suddenly, a can of worms was opened and the entire forum changed into a ‘battle-field’ on the issue of Mahdi and later ended in a debate on fundamentaldifferences between Sunna and Shi’ah.But let it be understood clearly, right from the on-set,that I am totally opposed to the debate. And to me, the articles written on the Mahdiand subsequentrejoinders to it, are not worth our precious time for several reasons, some of which are that some of the write-ups – especially of the person proposing the Shi’iteMahdi, lack any scholarship and academic values, for it isclear that it was copied from a book authored by someoneelse, although he does not even have thecourtesy to acknowledge the author. Of course this is a serious crime in academic cycles known as plagiarism. This fact is vividly clear to anybody who reads thesaid articles, for example at certain instances it states: ‘…as you would come to see in this book …’! And at other instances a reference is made to a footnote butno trace of it is found, whereas in other places the footnotes carry references tothe translator – of course none of us needs him to copy and force it down ourthroats and expect us to swallow it – hook, line and sinker – we can always go to any bookshop and buy the books and see for ourselves.In addition, even the source from which he copies lacks any authority because it contains multiples of errors, misrepresentations and distortions of facts. Forexample, in the first article alone, there are more than a dozen things attributed to Allah, the Prophet e and the authentic books of Sunnah which are but merefabrications as you will cometo see in this article (or may have already noticed). In factsome of these may negate one’s faith such as saying (about the Mahdi) :“during this period, the people could refer their problems to him and receivehis replies through his vicegerents” and that “for theultimate salvation of mankind, heis the Pole Star of hope on which the gaze of humanity is fixed” (compare this with the Christian belief in Jesus!!). Of course there is noneed to mention theabsurdities he wrote and claimed to be a definition and description of Ahlus Sunnah.On the other hand, the idea that there are authentic traditions of the prophet, if taken literary, will contradict the Qur’an and history etc, is wrong and apparentto anybody who has the leastunderstanding of the scienceof Hadith and explanations of the experts in this field. It is not by rejecting the authentic ahadeeth ofthe Prophet that we establishthe fallacies contained in Shi’ism, and particularly in the concept of their Mahdi.Thus let it be clearly understood that the coming of Mahdi, Isa (A.S.), Dajjal and other unseen prophecies are unquestionable facts established by the Qur’an andthe authentic Hadiths.(( ﻟﻮ ﻟﻢ ﻳﺒﻖ ﻣﻦ ﺍﻟﺪﻧﻴﺎ ﺇﻻ ﻳﻮﻡ ﻟﻄﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻴﻮﻡ ، ﺣﺘﻰ ﻳﺒﻌﺚ ﻓﻴﻪ ﺭﺟﻼً ﻣﻨﻲ ﺃﻭ ﻣﻦ ﺃﻫﻞ ﺑﻴﺘﻲ ، ﻳﻮﺍﻃﺊ ﺍﺳﻤﻪ ﺍﺳﻤﻲ ، ﻭﺍﺳﻢ ﺃﺑﻴﻪ ﺍﺳﻢ ﺃﺑﻲ ، ﻳﻤﻸ ﺍﻷﺭﺽﻗﺴﻄﺎً ﻭﻋﺪﻻً ﻛﻤﺎﻣﻠﺌﺖ ﻇﻠﻤﺎً ﻭﺟَﻮﺭﺍً (( ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ ﻭﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ﻭﺃﺣﻤﺪ ﻭﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻓﻲﺍﻟﻜﺒﻴﺮ ﻭﺍﻟﺼﻐﻴﺮ ﻭﺃﺑﻮ ﻧﻌﻴﻢ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﻠﻴﺔ .((Even if nothing remains of this world except a day, Allahwill prolong that day till he sends in it a man from my progeny or from my family (Ahlul-Bayt). He willbear my name, and the name of his father will be thesame as the name of my father. He will fill the world with justice and equity as it has been filled withinjustice.)) Reported by Abu Dawud (2/207), and also Tirmizi, Ahmad, Tabarani and Abu Nu’aim.And that these issues are in no way contradictory nor in any disagreement with any text of the Qur’an, but rather those doubting them are either ignorant of theauthentic view or have misconceptions about them – of course water may taste bitter to a feverish person – but who is to blame? The Prophet e said “The cure ofignorance is to ask” (those who know).But to say, as the Shi’ites will want us to believe, that Mahdi is existing in occultation for almost 1200 years and other such fairy tales, is but a mockery of Islamand is far from what Islam refers to on Mahdi, although this issue will be dealt with atan appropriate time in sha Allah.Now let it be understood thatthe Mahdi issue is neither the right topic to start with nor is it the bone of contention between Shi’ah and other muslims. And asstated earlier the so called ‘debate’ on certain issues between Shi’ah and Sunnah is a complete waste of time, a complete waste of efforts and a misplacement ofpriorities out of which no fruits will come. I am sure those sincere minds like that of Br. Sulaiman Aremu and others will agree with me, especially after followingthe debate to where it stands. My reasons for rejecting this kind of debate are :1. That the sources of the Shi’ites are totally different from those of other muslims, both in Creed and Jurisdiction, because the book in which every muslim’sbelief is built, that is, the Qur’an is doubted by the twelver Shi’ites. The Sunnah believed in by the muslims isnot accepted by the Shi’ah except a tiny fractionthereof, and consequently they have other sources that are unique to them among all muslims, some of which are : sayings of their Imams, Al-Jafr, Mushaf-Fatimah, and scriptures revealed to their Imams, andother sources of deriving jurisdiction.2. As a result of what is mentioned in No. 1, the Shi’ites differ from all muslims in their fundamental articles of creed which are unique and peculiar to them fromthe time of those disputes that occurred in the early centuries of Islam, and are never in agreement with any of the muslim sects on these particular issues. Howcan it be possible now in the fifteenth Islamic century that such agreements be reachedthrough debates like this, where most – if not all – of the audience as wellas the participants are not equal to this kind of task. By this I mean :3. Most of the subscribers in this forum are not known to be specialised in Islamic studies, but rather they are agroup of respected and honourable Nigerians, withkeen interest in knowing and practising Islam, and some civilised intellectuals educated in various professions (may Allah reward all of them with paradise). Althoughthat does not mean they are ignorant of Islam, but we should know that issues of this nature should not be regarded like current affairs where everyone has whatto say, professionals and lay men alike.4. Debates like this – if there is any need of it – should be between experts from both sides in a separate forum, that is on private e-mail addresses, the result ofwhich will later be made known to the NMN and its members. And the medium of communication should

Reply

nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

HISTORY OF ISLAMIC THEOLOGY (I)

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:04 PM

Bismillahir Rahmanir RahimAll praise is due to Allah, we praise Him and seek His assistance and guidance. We repent unto Him and seek His protection against the evils of our souls and that ofour bad deeds. Whomever Allah guides none can mislead, and whomsoever He misleads none can guide. I bear witness that there is none worthy of being worshipedexcept Allah, alone without partner, and I bear witness that Muhammad is His servant and messenger. MayAllah’s peace and blessings be bestowed upon him and hispure family and noble companions.((O ye who believe, fear Allahas He ought to be feared anddie not except as Muslims))((O mankind fear your Lord who created you from a single soul, and from it its mate and from the two of them scattered many males and females, fear Allah inwhose Name you beg one another, and (be mindful of) your kinship, most certainly Allah keeps a watch over you)).((O ye who believe, fear Allahand say that which is straight(and true), He will correct, for you, your deeds and forgive your sins, whoever obeys Allah and Hismessenger has certainly succeeded a great success)).As a new member of this forum, I have taken time observing the different write-ups from fellow brothers in the NMN, and was waiting for the time it will be ripeto start writing on issues thatwill be of benefit to all – bothreligiously and in their various fields of endeavour, issues that no muslim living today can afford tobe ignorant of, if he really wants to succeed in life and his role as a vicegerent of Allah on earth; and issues which unfortunately nobody seems to be turningattention to, much-less writing about.Suddenly, a can of worms was opened and the entire forum changed into a ‘battle-field’ on the issue of Mahdi and later ended in a debate on fundamentaldifferences between Sunna and Shi’ah.But let it be understood clearly, right from the on-set,that I am totally opposed to the debate. And to me, the articles written on the Mahdiand subsequentrejoinders to it, are not worth our precious time for several reasons, some of which are that some of the write-ups – especially of the person proposing the Shi’iteMahdi, lack any scholarship and academic values, for it isclear that it was copied from a book authored by someoneelse, although he does not even have thecourtesy to acknowledge the author. Of course this is a serious crime in academic cycles known as plagiarism. This fact is vividly clear to anybody who reads thesaid articles, for example at certain instances it states: ‘…as you would come to see in this book …’! And at other instances a reference is made to a footnote butno trace of it is found, whereas in other places the footnotes carry references tothe translator – of course none of us needs him to copy and force it down ourthroats and expect us to swallow it – hook, line and sinker – we can always go to any bookshop and buy the books and see for ourselves.In addition, even the source from which he copies lacks any authority because it contains multiples of errors, misrepresentations and distortions of facts. Forexample, in the first article alone, there are more than a dozen things attributed to Allah, the Prophet e and the authentic books of Sunnah which are but merefabrications as you will cometo see in this article (or may have already noticed). In factsome of these may negate one’s faith such as saying (about the Mahdi) :“during this period, the people could refer their problems to him and receivehis replies through his vicegerents” and that “for theultimate salvation of mankind, heis the Pole Star of hope on which the gaze of humanity is fixed” (compare this with the Christian belief in Jesus!!). Of course there is noneed to mention theabsurdities he wrote and claimed to be a definition and description of Ahlus Sunnah.On the other hand, the idea that there are authentic traditions of the prophet, if taken literary, will contradict the Qur’an and history etc, is wrong and apparentto anybody who has the leastunderstanding of the scienceof Hadith and explanations of the experts in this field. It is not by rejecting the authentic ahadeeth ofthe Prophet that we establishthe fallacies contained in Shi’ism, and particularly in the concept of their Mahdi.Thus let it be clearly understood that the coming of Mahdi, Isa (A.S.), Dajjal and other unseen prophecies are unquestionable facts established by the Qur’an andthe authentic Hadiths.(( ﻟﻮ ﻟﻢ ﻳﺒﻖ ﻣﻦ ﺍﻟﺪﻧﻴﺎ ﺇﻻ ﻳﻮﻡ ﻟﻄﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻴﻮﻡ ، ﺣﺘﻰ ﻳﺒﻌﺚ ﻓﻴﻪ ﺭﺟﻼً ﻣﻨﻲ ﺃﻭ ﻣﻦ ﺃﻫﻞ ﺑﻴﺘﻲ ، ﻳﻮﺍﻃﺊ ﺍﺳﻤﻪ ﺍﺳﻤﻲ ، ﻭﺍﺳﻢ ﺃﺑﻴﻪ ﺍﺳﻢ ﺃﺑﻲ ، ﻳﻤﻸ ﺍﻷﺭﺽﻗﺴﻄﺎً ﻭﻋﺪﻻً ﻛﻤﺎﻣﻠﺌﺖ ﻇﻠﻤﺎً ﻭﺟَﻮﺭﺍً (( ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ ﻭﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ﻭﺃﺣﻤﺪ ﻭﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻓﻲﺍﻟﻜﺒﻴﺮ ﻭﺍﻟﺼﻐﻴﺮ ﻭﺃﺑﻮ ﻧﻌﻴﻢ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﻠﻴﺔ .((Even if nothing remains of this world except a day, Allahwill prolong that day till he sends in it a man from my progeny or from my family (Ahlul-Bayt). He willbear my name, and the name of his father will be thesame as the name of my father. He will fill the world with justice and equity as it has been filled withinjustice.)) Reported by Abu Dawud (2/207), and also Tirmizi, Ahmad, Tabarani and Abu Nu’aim.And that these issues are in no way contradictory nor in any disagreement with any text of the Qur’an, but rather those doubting them are either ignorant of theauthentic view or have misconceptions about them – of course water may taste bitter to a feverish person – but who is to blame? The Prophet e said “The cure ofignorance is to ask” (those who know).But to say, as the Shi’ites will want us to believe, that Mahdi is existing in occultation for almost 1200 years and other such fairy tales, is but a mockery of Islamand is far from what Islam refers to on Mahdi, although this issue will be dealt with atan appropriate time in sha Allah.Now let it be understood thatthe Mahdi issue is neither the right topic to start with nor is it the bone of contention between Shi’ah and other muslims. And asstated earlier the so called ‘debate’ on certain issues between Shi’ah and Sunnah is a complete waste of time, a complete waste of efforts and a misplacement ofpriorities out of which no fruits will come. I am sure those sincere minds like that of Br. Sulaiman Aremu and others will agree with me, especially after followingthe debate to where it stands. My reasons for rejecting this kind of debate are :1. That the sources of the Shi’ites are totally different from those of other muslims, both in Creed and Jurisdiction, because the book in which every muslim’sbelief is built, that is, the Qur’an is doubted by the twelver Shi’ites. The Sunnah believed in by the muslims isnot accepted by the Shi’ah except a tiny fractionthereof, and consequently they have other sources that are unique to them among all muslims, some of which are : sayings of their Imams, Al-Jafr, Mushaf-Fatimah, and scriptures revealed to their Imams, andother sources of deriving jurisdiction.2. As a result of what is mentioned in No. 1, the Shi’ites differ from all muslims in their fundamental articles of creed which are unique and peculiar to them fromthe time of those disputes that occurred in the early centuries of Islam, and are never in agreement with any of the muslim sects on these particular issues. Howcan it be possible now in the fifteenth Islamic century that such agreements be reachedthrough debates like this, where most – if not all – of the audience as wellas the participants are not equal to this kind of task. By this I mean :3. Most of the subscribers in this forum are not known to be specialised in Islamic studies, but rather they are agroup of respected and honourable Nigerians, withkeen interest in knowing and practising Islam, and some civilised intellectuals educated in various professions (may Allah reward all of them with paradise). Althoughthat does not mean they are ignorant of Islam, but we should know that issues of this nature should not be regarded like current affairs where everyone has whatto say, professionals and lay men alike.4. Debates like this – if there is any need of it – should be between experts from both sides in a separate forum, that is on private e-mail addresses, the result ofwhich will later be made known to the NMN and its members. And the medium of communication should

Reply

nuramuhd3
Admin

36, male

Posts: 118

HISTORY OF ISLAMIC THEOLOGY (I)

from nuramuhd3 on 04/26/2015 11:01 PM

Bismillahir Rahmanir RahimAll praise is due to Allah, we praise Him and seek His assistance and guidance. We repent unto Him and seek His protection against the evils of our souls and that ofour bad deeds. Whomever Allah guides none can mislead, and whomsoever He misleads none can guide. I bear witness that there is none worthy of being worshipedexcept Allah, alone without partner, and I bear witness that Muhammad is His servant and messenger. MayAllah’s peace and blessings be bestowed upon him and hispure family and noble companions.((O ye who believe, fear Allahas He ought to be feared anddie not except as Muslims))((O mankind fear your Lord who created you from a single soul, and from it its mate and from the two of them scattered many males and females, fear Allah inwhose Name you beg one another, and (be mindful of) your kinship, most certainly Allah keeps a watch over you)).((O ye who believe, fear Allahand say that which is straight(and true), He will correct, for you, your deeds and forgive your sins, whoever obeys Allah and Hismessenger has certainly succeeded a great success)).As a new member of this forum, I have taken time observing the different write-ups from fellow brothers in the NMN, and was waiting for the time it will be ripeto start writing on issues thatwill be of benefit to all – bothreligiously and in their various fields of endeavour, issues that no muslim living today can afford tobe ignorant of, if he really wants to succeed in life and his role as a vicegerent of Allah on earth; and issues which unfortunately nobody seems to be turningattention to, much-less writing about.Suddenly, a can of worms was opened and the entire forum changed into a ‘battle-field’ on the issue of Mahdi and later ended in a debate on fundamentaldifferences between Sunna and Shi’ah.But let it be understood clearly, right from the on-set,that I am totally opposed to the debate. And to me, the articles written on the Mahdiand subsequentrejoinders to it, are not worth our precious time for several reasons, some of which are that some of the write-ups – especially of the person proposing the Shi’iteMahdi, lack any scholarship and academic values, for it isclear that it was copied from a book authored by someoneelse, although he does not even have thecourtesy to acknowledge the author. Of course this is a serious crime in academic cycles known as plagiarism. This fact is vividly clear to anybody who reads thesaid articles, for example at certain instances it states: ‘…as you would come to see in this book …’! And at other instances a reference is made to a footnote butno trace of it is found, whereas in other places the footnotes carry references tothe translator – of course none of us needs him to copy and force it down ourthroats and expect us to swallow it – hook, line and sinker – we can always go to any bookshop and buy the books and see for ourselves.In addition, even the source from which he copies lacks any authority because it contains multiples of errors, misrepresentations and distortions of facts. Forexample, in the first article alone, there are more than a dozen things attributed to Allah, the Prophet e and the authentic books of Sunnah which are but merefabrications as you will cometo see in this article (or may have already noticed). In factsome of these may negate one’s faith such as saying (about the Mahdi) :“during this period, the people could refer their problems to him and receivehis replies through his vicegerents” and that “for theultimate salvation of mankind, heis the Pole Star of hope on which the gaze of humanity is fixed” (compare this with the Christian belief in Jesus!!). Of course there is noneed to mention theabsurdities he wrote and claimed to be a definition and description of Ahlus Sunnah.On the other hand, the idea that there are authentic traditions of the prophet, if taken literary, will contradict the Qur’an and history etc, is wrong and apparentto anybody who has the leastunderstanding of the scienceof Hadith and explanations of the experts in this field. It is not by rejecting the authentic ahadeeth ofthe Prophet that we establishthe fallacies contained in Shi’ism, and particularly in the concept of their Mahdi.Thus let it be clearly understood that the coming of Mahdi, Isa (A.S.), Dajjal and other unseen prophecies are unquestionable facts established by the Qur’an andthe authentic Hadiths.(( ﻟﻮ ﻟﻢ ﻳﺒﻖ ﻣﻦ ﺍﻟﺪﻧﻴﺎ ﺇﻻ ﻳﻮﻡ ﻟﻄﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻴﻮﻡ ، ﺣﺘﻰ ﻳﺒﻌﺚ ﻓﻴﻪ ﺭﺟﻼً ﻣﻨﻲ ﺃﻭ ﻣﻦ ﺃﻫﻞ ﺑﻴﺘﻲ ، ﻳﻮﺍﻃﺊ ﺍﺳﻤﻪ ﺍﺳﻤﻲ ، ﻭﺍﺳﻢ ﺃﺑﻴﻪ ﺍﺳﻢ ﺃﺑﻲ ، ﻳﻤﻸ ﺍﻷﺭﺽﻗﺴﻄﺎً ﻭﻋﺪﻻً ﻛﻤﺎﻣﻠﺌﺖ ﻇﻠﻤﺎً ﻭﺟَﻮﺭﺍً (( ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ ﻭﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ﻭﺃﺣﻤﺪ ﻭﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻓﻲﺍﻟﻜﺒﻴﺮ ﻭﺍﻟﺼﻐﻴﺮ ﻭﺃﺑﻮ ﻧﻌﻴﻢ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﻠﻴﺔ .((Even if nothing remains of this world except a day, Allahwill prolong that day till he sends in it a man from my progeny or from my family (Ahlul-Bayt). He willbear my name, and the name of his father will be thesame as the name of my father. He will fill the world with justice and equity as it has been filled withinjustice.)) Reported by Abu Dawud (2/207), and also Tirmizi, Ahmad, Tabarani and Abu Nu’aim.And that these issues are in no way contradictory nor in any disagreement with any text of the Qur’an, but rather those doubting them are either ignorant of theauthentic view or have misconceptions about them – of course water may taste bitter to a feverish person – but who is to blame? The Prophet e said “The cure ofignorance is to ask” (those who know).But to say, as the Shi’ites will want us to believe, that Mahdi is existing in occultation for almost 1200 years and other such fairy tales, is but a mockery of Islamand is far from what Islam refers to on Mahdi, although this issue will be dealt with atan appropriate time in sha Allah.Now let it be understood thatthe Mahdi issue is neither the right topic to start with nor is it the bone of contention between Shi’ah and other muslims. And asstated earlier the so called ‘debate’ on certain issues between Shi’ah and Sunnah is a complete waste of time, a complete waste of efforts and a misplacement ofpriorities out of which no fruits will come. I am sure those sincere minds like that of Br. Sulaiman Aremu and others will agree with me, especially after followingthe debate to where it stands. My reasons for rejecting this kind of debate are :1. That the sources of the Shi’ites are totally different from those of other muslims, both in Creed and Jurisdiction, because the book in which every muslim’sbelief is built, that is, the Qur’an is doubted by the twelver Shi’ites. The Sunnah believed in by the muslims isnot accepted by the Shi’ah except a tiny fractionthereof, and consequently they have other sources that are unique to them among all muslims, some of which are : sayings of their Imams, Al-Jafr, Mushaf-Fatimah, and scriptures revealed to their Imams, andother sources of deriving jurisdiction.2. As a result of what is mentioned in No. 1, the Shi’ites differ from all muslims in their fundamental articles of creed which are unique and peculiar to them fromthe time of those disputes that occurred in the early centuries of Islam, and are never in agreement with any of the muslim sects on these particular issues. Howcan it be possible now in the fifteenth Islamic century that such agreements be reachedthrough debates like this, where most – if not all – of the audience as wellas the participants are not equal to this kind of task. By this I mean :3. Most of the subscribers in this forum are not known to be specialised in Islamic studies, but rather they are agroup of respected and honourable Nigerians, withkeen interest in knowing and practising Islam, and some civilised intellectuals educated in various professions (may Allah reward all of them with paradise). Althoughthat does not mean they are ignorant of Islam, but we should know that issues of this nature should not be regarded like current affairs where everyone has whatto say, professionals and lay men alike.4. Debates like this – if there is any need of it – should be between experts from both sides in a separate forum, that is on private e-mail addresses, the result ofwhich will later be made known to the NMN and its members. And the medium of communication should strictly be the language in which original Islamic books arewritten, that is the arabic language, to avoid misapprehensions that reallyoccur in translations.5. Brothers should not wastetheir talents debating upon some topics selected by the Shi’ites intentionally to createan amount of doubt in the minds of muslims asregards their sources. For one thing many do not observe is that Shi’ite attacks on the Sunnis is mostly – if not always – on either the authenticity of the Qur’an,that is by reminding you that this Qur’an was collected andwritten in the final form of a book in the time of the first caliphs, Abubakar, Umar andespecially inthe reign of Uthman in whichit was compiled and distributed to all muslim countries – or the authenticity of the Sunnah and that is by making you believe that theSahaba through whom we received the whole of this religion are infidels, not trustworthy etc., the result ofwhich is either a total negation of anything narratedby them or at least doubting its authenticity. This I will discuss in more detail- in shaAllah – under the topic of theShi’ites stand on the Sahaba, and their conceptof ‘ismah (infallibility) of the Imams.6. The best thing therefore is for the muslim ummah to know who these people are, what they carry with them asreligion, where they are heading to, what theircreeds and beliefs are built on, who their predecessors are after alienating the companions of the prophet e, are they true lovers of the Ahl-Bayt etc.Thus by virtue of my specialisation, I have a humble contribution to makein this field, in the form of objective and fair research. I had done a detailed researchon the various sects in Islam and their historical origins, both existing and those that have died out with the passage of time, and I was intending to present a briefsummary of this research to my fellow brothers in this forum, when the issue of Shi’ism came up. Thus I havedecided to start by giving a detailed discussion onShi’ah right from the time of its conception and delivery up to its present day manifestation, in an objective and scholarly manner, vowing not to mention anythingbelieved by the Shi’ites but from their authentic books generally accepted and recognized by their mullahs. Later on, in sha Allah, I can go back to other parts ofthe topic in a series of articles. This, I believe, will be more useful to members who really want to know.**NOTEThis is a series of artices written by the Sheikh, as a sincere reminder to the (Nigeria Muslim Forum) way back in 2008.

Reply
First Page  |  «  |  1  |  2  |  3  |  4  |  5  |  6  ...  24  |  »  |  Last

« Back to previous page